Buhari ya roki yan bindigan Niger Delta

Buhari ya roki yan bindigan Niger Delta

- Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa Najeriya na kashe dala biliyan 22 a duk shekara gurin shigo da alkama, shinkafa, sikari da kuma kifi amma idan yan bindiga suka sauke makamansu suka kuma koma gona, abubuwa zasu canja kan tattalin arziki

- Buhari yace aiki tare da gwamnati ta wannan fanni zai ceto matasa daga rashin aiki, kare al’umma, ci gaban zaman lafiya da kuma hannun jari da Karin kudin shiga a jihohin Niger Delta.

Buhari ya roki yan bindigan Niger Delta
Shugaban kasa Muhammad Buhari ya roki yan bindigan Niger Delta da su ajiye makamai

Shugaban kasa Muhammad Buhari ya roki yan bindigan Nigerr Delta da s daina fashe-fashen bututunan mai su kuma rungumi zaman lafiya.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa shugaban kasa yayi wannan roko ne a ranar Asabar, 19 ga watan Nuwamba a grin taron cikar kamfanin man Agip ashekaru 20 a Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa.

KU KARANTA KUMA: Dan shekara 60 yayi wa budurwa fyade a Abia (hotuna)

Shgaban kasar, wanda ministan jiha kan harkan noma da ci gaban karkara Sanata Hwineken Lokpobiri ya wakilce shi, yace yan bindigana s rungumi zaman lafiya da kuma mayar da hankali a kan aikin noma don daidaituwar ci gaban tattalin arziki da samar da dukiya.

A yan makonni da suka wuce, kokarin da gwamnatin tarayya tayi don gannin ta samu yan bindigan sn daina lalata bututunan mai bai yi nasara ba duk da tattaunawa da akeyi a tsakanin kungiyoyin guda biyu.

Yan bindigan sun yi ikirarin cewa dalilin su na kin dakatar da fashe-fashen ya kasance saboda suna son dakatar da gwamnati daga daukan su da rashin muhimmanci a lokacin tattaunawan. Zuwa yanzu, dattawan Niger Delta a tattanawa  sun ba gwamnatin tarayya bukatun su.

Ku biyo shafinmu na Tuwita: @naijcomhausa.

https://youtu.be/D_Sg8sXjJcM

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng