Jiga-Jigan malaman Saudiyya sun kawo ma Buhari ziyara

Jiga-Jigan malaman Saudiyya sun kawo ma Buhari ziyara

- Manyan baki sun shigo Najeriya a yau

- Babban limamin Masallacin Madina ya kawo ma Shugaba Muhammadu Buhari ziyara

Jiga-Jigan malaman Saudiyya sun kawo ma Buhari ziyara

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tarbi Babban limamin Masallacin Madina,saudiyya a fadar shugaban kasa a yau, juma’a,7 ga watan Oktoba.

KU KARANTA: Ghana ta fara fidda mai zuwa Najeriya da kasashen Afrika ta yamma

Shugaba Buhari ya tarbi gwamnan jihar Zamfara, Abubakar Yari, Babban Limamin Masallacin Madina Sheik Abdul-Muhsin Ibn Muhammad Al-Kasimy, jakadan Saudiyya , Majeed BN Muhammed Algahtamy da Malam Awwal a Aso villa a yau.

Daga cikin jiga-jigan malaman Najeriyan da suka taka ma limamin baya sune, Shugaban Kungiyar JIBWIS, Shaykh Abdullahi Bala Lau; Sakataran Kungiyar JIBWIS,Shayk Muhammad Kabiru Haruna Gombe da sauran su.

Jiga-Jigan malaman Saudiyya sun kawo ma Buhari ziyara

Wasu suna tuhumar Shugaba Buhari da yunkurin musulantar da Najeriya saboda yana nada musulmai a manyan matsayoyi, yana azabtar da mutanen kudu da kuma kashe-kashen da Fulani makiyaya keyi da sauran su.

Shi kuma Shugaba Buhari da yake mutum ne mai basira, bai amsa masu gurnanin ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng