Jihar Zamfara
A labarin nan, za a ji cewa dan majalisa ar tarayya daga jihar Zamfara, Aminu Sani Jaji ya bayar da tabbacin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai yi nasara a 2027.
Kungiyar dattawan Arewa ta jam’iyyar PDP ta zargi Ministan Tsaron Ƙasa, Bello Matawalle, da lalata jam’iyyar ta hanyar janyo mambobi su koma APC.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa zaben Kabiru Tanimu Turaki a matsayin wanda suke goyon bayan ya zama shugaban PDP ya halatta a doka.
Jiga-jigan jam'iyyar PDP 15 a Zamfara, ciki har da shugabanni na jiha, sun koma APC. Yari da Matawalle za su karɓe su, APC ta ce za ta kwato mulki a 2027.
Dakarun rundunar sojojin Najeriya sun yi artabu da 'yan bindiga a jihar Zamfara. Sojojin sun samu nasarar fatattakar 'yan bindigan wadanda suka zo daukar fansa.
Dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe dan ta'adda, Abu AK a jihar Zamfara. An kashe dan ta'addan ne yayin da ya shiga cin kasuwa a karamar hukumar Tsafe.
Jagoran 'yan ta'adda, Bello Turji ya saki sama da mutum 100 a kokarin kawo zaman lafiya a Najeriya. Ana kokarin sulhu da Turji domin daina kai hare hare Zamfara.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun yi awon gaba da mutane masu yawa a wasu hare-haren da suka kai a jihar Zamfara. Sun tafi da su cikin daji.
Wasu 'yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hari a jihar Zamfara inda suka yi awon gaba da mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba.
Jihar Zamfara
Samu kari