Jihar Zamfara
An samu tashin wata mummunar gobara a wata babbar kasuwa da ke birnin Gusau a jihar Zamfara. Gobarar ta lakume shaguna masu yawa a kasuwar ta babura.
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa ya amince da gina filin jirgin saman kasa da ƙasa ne domin ta haka ne kaɗai masu zuba jari za su zo jihar.
Bullar ƙungiyar Lakurawa a yankin Arewa maso Yamma na zama babban barazana ga shugabannin yan bindiga wanda ka iya zama tashin hankali tsakaninsu.
Rikakken dan ta'adda, Bello Turji ya yi barazanar daukar munanan matakai na kai hare-hare a wasu yankunan Sokoto da Zamfara idan ba a sako abokinsa da aka cafke ba.
Sojojin Najeriya sun kama hatsabibin shugaban 'yan bindiga Bako Wurgi, wanda ke da alhakin kisan sarkin Gobir, yayin da yake jinya a asibitin Shinkafi.
‘Yan bindiga biyu sun gamu da ajalinsu a garin gwajin bam a sansanin Bello Turji. Fashewar bam din tatilasta mazauna Garin Gwale guduwa daga gidajensu a Zamfara.
Dakarun sojojin Najeriya tare da hadin gwiwar 'yan banga sun yi arangama da 'yan ta'adda a jihar Zamfara. Sojojin sun hallaka 'yan ta'adda tare da kwato makamai.
Ksramin ministan tsaron Najeriya ya nuna goyon bayansa kan kudirin haraji na gwamntin Bola Tinubu. Ya yaba da manufofinsa kan tattalin arzikin kasar nan.
Gwamnatin jihar Zamfara ta kaddamar da raba tallafin kudi har Naira biliyan 4.9. Mata, marasa lafiya, 'yan agaji da malaman Islamiyya za su samu tallafin.
Jihar Zamfara
Samu kari