Jihar Zamfara
Kakakin jam'iyyar APC a jihar Zamfara ya bayyana cewa katin Bello Turji na jam'iyyar na bogi ne. Yusuf Idris ya ce Bello Turji ba dan jam'iyyar APC ba ne.
'Yan bindiga dauke da makamai sun yi wa jami'an tsaro na sojoji kwanton bauna a jihar Zamfara. An samu asarar rayuka bayan an gwabza fada tsakanin bangarorin biyu.
Harin 'yan bindiga a Zamfara ya jefa Shugaban Karamar Hukumar Tsafe da tawagarsa cikin fargaba, yayin da suke kan hanya don ceto mutane daga masu garkuwa.
Nazarin dambarwar siyasar 2027 a jihohin Kano, Rivers, da wasu jihohi 3 gabanin 2027; sauya shekar Fubara da dambarwar Abba Kabir Yusuf da Kwankwaso a Kano.
Ministan Tsaro na Kasa, Bello Matawalle, na shirin aurar da ’ya’yansa tara a Abuja. Bikin zai gudana a Masallacin Kasa a ranar 6 ga Fabrairun 2026.
Wasu matafiya sun taka bam da ake zargin 'yan ta'adda sun dasa a jihar Zamfara. Lamarin ya jawo an samu jikkatar mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
Jam'iyyar APC a Zamfara ta karyata rahoton cewa Gwamna Dauda Lawal ya aika da wasikar sauya sheka, tana zargin labarin a matsayin kirkirarre da yaudara.
Waau miyagun 'yan bindiga sun kai farmaki kasuwar Daji da ke yankin karamar hukumar Kauran Namoda a jihar Zamfara, sun yi awon gaba da shanu fiye da 500.
Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Abdullahi Fodio a Kebbi za ta karrama Gwamna Nasir Idris da digirin girmamawa, tare da yaye dalibai 7,221 a taron tarihi.
Jihar Zamfara
Samu kari