Yar Makaranta
Hukumar kula da ƙananan yara ta UNICEF ta fitar da wani rahoto inda ta gano Kanuri, Fulani, da Hausa sun fi fama da yaran da ba su zuwa makaranta a Najeriya a 2024.
Ilimi a Arewa Najeriya na cikin mawuyacin hali saboda rashin tsaro, talauci, da al’adu, inda miliyoyin yara musamman mata ke rasa damar zuwa makaranta.
Gwamna Umaru Bago zai rika daukar nauyin karatun mata 1,000 duk shekara domin karanta fannin lafiya. Zai raba kwanfutoci miliyan 1 a makarantun gwamnati.
'Yar shekara 15, Miss Hussaina Adam da ta zama gwamnan jihar Kaduna ta kwana daya ta yiwa yaran jihar alkawarin ba su ingantaccen ilimi da kuma kare hakkokinsu.
Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da fara ba da ilimi kyauta har zuwa matakin sakandare daga Janairu 2025, domin inganta ilimi ga dukkanin yara a jihar.
Majalisar dattawan kasar nan ta ce ana kokarin daukar hukunci a kan iyayen da ba sa sanya yaransu a makaranta, za a bijiro da kudurin daure iyaye ma watanni shida.
Jami’an ‘yan sandan jihar Bauchi sun kama wasu daliban makarantar sakandare biyu bisa zargin satar wayoyin hannu guda 100 da na’urorin lantarki a wani shago.
Makarantar Firamare ta Okugbe, Ikpide-irri, tana da malami daya tilo da ke koyar da dalibai sama da 170 wanda ya sa al'ummar yankin suka garzaya ofishin gwamnati.
Isabel Anani, 'yar shekara 16 mai fafutukar daidaiton jinsi ta zama shugabar majalisar wakilai na wucin gadi yayin da ake bikin 'ranar 'ya'ya mata ta duniya.'
Yar Makaranta
Samu kari