Albashin ma'aikata
Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq ya amince a fara biyan ma'aikatan gwamnatinsa sabon albashi mafi ƙaranci na N70,000 a watan Oktoba, 2024.
Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas ya bi layin gwamnan Legas, ya amince da N85,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikatan gwamnati.
Sanata Orji Kalu, ya bayyana abin da yake samu duk wata a matsayinsa na dan majalisar tarayya. Hakan ya biyo bayan wani Sanata ya ce yana karbar N21m duk wata.
Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ce a watan Janairu, 2025, gwamnatinsa za ta fara biyan N100,000 ga ma'aikata a matsaƴin albashi mafi ƙaranci a jihar Legas.
Gwamnatin jihar Lagos ta amince da biyan mafi ƙarancin albashin N85,000 inda Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ce zai kara mafi ƙarancin albashin zuwa N100,000.
Yayin da ma'aikata ke cikin halin kunci a Najeriya, Gwamnatin jihar Delta ta shirya biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 a karshen wannan wata ta Oktoba.
Gwamnan Ekiti, Biodun Oyebanji, ya karawa wasu hazikan ma’aikatan gwamnati 82 kyautar N42m tare da ba su tabbacin biyan N70,000 a matsayin mafi karancin albashi.
An tattara jerin gwamnonin Najeriya da ke biyan mafi karancin albashi fiye da na gwamnatin tarayya. An yi mamaki yadda gwamnatin Gombe za ta biya fiye da N70,000.
Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya dakatar da hadiminsa bayan ya yi ikirarin cewa ya amince zai biya ma'aikata sabon mafi karancin albashi na N70,000.
Albashin ma'aikata
Samu kari