Albashin ma'aikata
Ministan Kwadago, Dingyadi, ya bayyana cewa gwamnati za ta hana shiga yajin aiki ta hanyar tattaunawa da 'yan kwadago da samar da hanyoyin warwarewar matsaloli.
Gwamnatin jihar Kaduna ta fara biyan sabon mafi karancin albashi na N72,000 ga ma'aikatan jihar a watan Nuwamba. Gwamnati na jiran koke daga ma'aikata.
Gwamantin Jigawa ta ayyana N70,000 a mafi ƙarancin albashi. Za a rika ba ma'aikata bashin suna noma tare da rage musu farashin kayan abinci a shaguna.
Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya fara biya ma'aikata mafi karancin albashin N85,000 kamar yadda ya yi alkawari a baya inda ma'aikatan suka yi godiya.
Kungiyoyin ma'aikata a Kano sun fara yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf bayan tabbatar da an fara biyan ma'aikata mafi karancin albashin N71,000 a fadin jihar.
Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta fara aiwatar da dokar sabon mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatanta a watan nan.
Gwamnan Imo, Hope Uzodimma ya sanar da amincewarsa na fara aiwatar da sabon mafi karancin albashin N70,000 ga ma'aikatan jihar. Ya karawa wasu albashi.
Kungiyar kwadago ta NLC ta umarci 'yan kungiyar a jihar Jigawa da sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani saboda gazawar gwamnati na fara biyan albashin N70,000.
Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da sabon mafi karancin albashi gama'aikatan jihar. Gwamnan ya amince a fara biyan sabon albashin daga watan Disamba.
Albashin ma'aikata
Samu kari