Albashin ma'aikata
Gwamnatin jihar Bauchi ta amince da karin albashi mai tsoka ga likitoci da ma'aikatan lafiya a fadin jihar. Ta amince da karin ne domin bunkasa ayyukansu.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya amince a biya ma'ikata albashin watan 13. Ya ce hakan na daga cikin abin da yake yo tun bayan hawansa mulki a shekarar 2019.
Gwamna Umo Eno ya tallafa wa mawakin yabo wanda ya kasance makaho Chris Vic da filin ƙasa, gida, da jarin N100m domin karfafa dogaro da kai a Akwa Ibom.
Kungiyar tsofaffin ma’aikatan gwamnatin tarayya ta sanar da shirin gudanar da zanga-zangar tsirara a fadin kasa saboda bashin karin fansho da tallafi.
Hukumar Kula da Harkokin Shari'a ta Jihar Kano ta dakatar da wani rijistara da babban jami'in kotu kan zarge-zargen aikata laifuffuka masu girma.
Kungiyar likitoci masu neman kwaewar aiki ta dakatar da yajin aikinta bayan kwanaki 29, inda ta bai wa gwamnati makonni hudu don aiwatar da bukatunta 19.
Kamfanin samar da wutar lantarki a Abuja (AEDC) ya fara sallamar ma’aikata kusan 800 bayan watanni na sake tsari a cikin gida wanda aka yi niyyar korar 1,800.
Kungiyar likitoci ta NARD ta fara yajin aiki na ƙasa baki ɗaya, inda take neman karin albashi, gyaran asibitoci, da inganta yanayin aiki don kare lafiyar jama’a.
Gwamnatin Imo ta fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na ₦104,000 ga ma’aikata, matakin da ya sanya ta kan gaba a Najeriya wajen inganta walwalar ma’aikata.
Albashin ma'aikata
Samu kari