Kudu maso gabashin Najeriya
Rahotanni sun bayyana cewa Sarkin Badagry, Aholu Toyi I ya tilastawa 'yan kasuwar Agbalata sauke farashin kayan abinci da sauran kayayyakin masarufi.
Majalisar Dattawan Yarabawa (YCE) ta bukaci gwamnatin tarayya da ta gaggauta daukar matakin saukakawa 'yan kasa bayan NNPCL ya sanar da karin kudin fetur.
Gwamnatin tarayya ta ce ambaliyar ruwa za ta iya yiwa wasu jihohi 21 illa a nan gaba kadan. Gwamnatin ta bayyana sunayen jihohi 7 da ambaliyar za ta fi yiwa barna.
Gwamnan jihat Ebonyi, Francis Nwifuru ya ce da zarar shugaban ma'aikata da ma'aikata sun cimma matsaya kan tsarin da za a bi, zai fara biƴan sabon albashi N70,000
Wasu yan bindiga da ake kyautata zaton ƴan aware ne sun kai hari hedkwatar ƴan sanda da ke ƙaramar hukumar Idemeli ta Kudu a jihar Anambra, sun kashe kofur.
Mun tattaro bayanan manyan sarakunan Najeriya 7 da suka rigamu gidan gaskiya a cikin watanni 8 na shekarar 2024 da muke ciki. Mutuwar Sarkin Gobir ta girgiza jama'a.
Tsohon shugaban jam'iyyar PDP a jihar Abia kuma Sanata, Emma Nwaka ya yi murabus daga jam'iyyar inda ya ce ya yi hakan ne saboda wasu dalilai a karan kansa.
Babbar kotun jihar Imo ta yi zama game da korafi da aka shigar kan gwamnati inda ta dakatar da Gwamna Hope Uzodinma daga shirin rushe babbar kasuwar Owerri.
Sabon rikici ya kunno a kai a APC reshen Benuwai yayin da tsagin kwamitin shugabancin rikon kwarya na Omale da na bangaren Austin Agada suka fara nunawa juna yatsa.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari