Kudu maso gabashin Najeriya
Tsohon hadimin Muhammadu Buhari ya shiga matsala da shugaban kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, ya kai kararsa kotu kan zargin bata masa suna da kiransa 'dan ta'adda.
NAHCON ta amince da Naira miliyan 8.7 a matsayin kudin aikin Hajjin 2025 ga maniyyatan Kudu, sai Naira miliyan 8.3 ga 'yan Arewa maso Gabas. Ta yi karin bayani.
Matar Benjamin Ezemma ta roƙi jami'an tsaro su gano mijinta da aka sace a Anambra, tana nuna damuwa game da yadda ake gudanar da bincike kan batansa.
Gwamnan Anambra, Soludo, ya kaddamar da rundunar tsaro ta "Udo Ga-Achi" tare da bayar da kyautar Naira miliyan 5 ga masu bayar da bayanai kan 'yan ta'adda.
Rahotanni sun tabbatar da cewa uwargidan tsohon gwamnan farko na jihar Delta, Olorogun Felix Ibru ta riga mu gidan gaskiya a birnin London da ke Burtaniya.
Majalisar dokokin Legas ta tsige Mudashiru Obasa saboda zargin rashin ɗa'a. Legit Hausa ta jero shugabannin majalisar jihohi da aka taba tsigewa.
Gwamnan Ondo ya ayyana ranar hutu don zaben kananan hukumomi, yayin da PDP ta janye saboda rashin amincewa da hukumar ODIEC. ‘Yan sanda sun takaita zirga-zirga.
Popoola Joshua, tsohon ɗan takarar NNPP a Oyo, ya koma APC don ƙarfafa jam’iyyar. Tuni Ganduje ya umarci APC ta yi tsare-tsare domin karɓar mulki daga PDP.
Gwamnonin Najeriya sun yi watsi da ƙarin VAT, sun gabatar da sabuwar hanyar rabon haraji don tabbatar da daidaito da kare talakawa, da goyon bayan ci gaban harajin.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari