Kudu maso gabashin Najeriya
Shugaban IPOB, Nnamdi Kanu ya roƙi kotu ta mayar da shi daga gidan yari na Sokoto zuwa yankin Abuja, yana cewa nisan wurin yana hana shi shirya daukaka kara.
An tsige shugaban jam'iyyar APC na jihar Cross River, Alphonsus Ogar Eba bayan kuri’ar rashin amincewa da mulkinsa bia zargin almundahana da rufe ofis.
Kungiyar NDYC daga Kudancin Najeriya ta roƙi Bola Ahmed Tinubu ya ƙi amincewa da yunkurin batanci da ake yi wa karamin ministan tsaro, Mohammed Matawalle.
Gwamnatin Abia ta karyata labarin da ake yadawa cewa Gwamna Alex Otti ya sha da kyar a harin yan bindiga, ta ce wadanda aka farmaki ba ayarin Gwamna ba ne.
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ayyana dokar hana fita ta sa’o’i 24 a garin Igbajo, da ke ƙaramar hukumar Boluwaduro bayan barkewar rikici.
Hatsarin mota ya kashe mutane shida a titin Awka–Onitsha da ke jihar Anambra bayan karo tsakanin tipa da bas da ke dawowa daga jana’iza a jihar Ebonyi
A makon da ya gabata ne aka yanke wa shugaban IPOB, Nnamdi Kanu hukuncin daurin fai da rai, ya shiga jerin wadanda suka wakilci kansu a kotu babu lauya.
Tsohon ministan kwadago, Dr. Chris Ngige, ya bayyana cewa yana nan a raye bayan wasu yan bindiga sun farmake shi a kan wani titi a jihar Anambra.
Wata mata ta rasa rayuwarta bayan ‘yan bindiga sun harbe ta yayin da take ɗaukar bidiyon harin da aka kai wa jerin gwanon motocin Chris Ngige a Anambra.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari