Kudu maso gabashin Najeriya
An kama mutum 1 bayan fashewar bam a sakatariyar jihar Bayelsa yau 11 ga Fabrairu, 2026. Babu wanda ya mutu, kuma ƴan sanda sun tabbatar da dawo da doka da oda.
Magidancin da aka sani da Iseleto ya kashe ɗansa mai shekara 23, Miracle, ta hanyar soka masa wuƙa a ranar Lahadi. Rundunar 'yan sanda ta fara neman mutumin.
Ƴan banga sun kai hari ofishin ADC a Benin; sun lalata kayayyaki tare da ƙoƙarin ƙona ginin da man fetur don tsoratar da jam'iyyar hamayya kafin zaɓen 2027.
TCN zai katse wuta a Ondo da Okitipupa daga 2 zuwa 5 ga Fabrairu, 2026, domin gudanar da aikin gyara a tashar Ife/Ondo don inganta rarraba wutar lantarki a yankin.
Gwamna Francis Nwifuru na Ebonyi ya rufe makarantu a Amasiri bayan harin da ya yi sanadin kisan mutane hudu, yana tabbatar da doka da oda a yankin.
Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasarta kan ziyartar jihohin Najeriya 18 saboda garkuwa da ta'addanci; ta bayyana Najeriya a matsayin wurin da ke da babban haɗari a 2026.
Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru ya dauki zafi kan harin da mutanen garin Amisiri suka kai kan mutanen Okporojo, wanda aka yi wa mutum hudu yankar rago.
Runduna ta 13 ta sojin Najeriya ta musanta zargin fyaɗe da karɓar kuɗi a Cross River; ta ce an shirya bidiyon da ake yadawa don yaudarar jama'a da bata sunan jami'ai
Ƙungiyar mata Musulmi ta yi gargaɗi kan barazana ga Musulman Igbo, musamman mata masu hijabi, tare da bayyana halin da mata masu nakasa ke ciki a yanzu.
Kudu maso gabashin Najeriya
Samu kari