
Siyasar Najeriya







Gwamnan jihar Akwa Ibom na jam'iyyar PDP, Umo Eno, ya bayyana matsayarsa kan takarar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027. Ya nuna goyon bayansa ga Tinubu.

Majalisar wakilai ta kafa kwamiti mai mutane 21 domin lura da harkokin majalisar dokokin Rivers da aka dakatar. Kwamitin zai lura da aikin da shugaban riko ke yi.

Wata kungiyar matasa ta bayyana cewa za ta hada kan mutane miliyan 5 domin nuna jin dadin mulkin Bola Tinubu a jihar Abia tare da goyon bayan Sanata Orji Kalu.

Dele Momodu ya ce kalubalantar Tinubu da Wike a 2027 tamkar gasar cin kofin duniya ce. Ya kuma soki gwamnonin PDP kan kin shiga kawancen hamayya.

Tsohon dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya dage cewa dole ne a hada kai don a karbe mulki daga Bola Tinubu a zaben shekarar 2027.

Taron jam'iyyar APC a Legas ya rikide zuwa rikici yayin da mambobi suka fusata kan kakaba dan takarar shugaban Ojokoro daga Agege, lamarin da suka ce ba su yarda ba.

Gwamnatin Binuwai ta kare kanta bayan tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi ya zarge ta da hana shi kai ziyarar jin kai sansanin 'yan gudun hijira da ke jihar.

Jigon PDP kuma mamba a kwamitin amintattu (BoT), Bode George ya bayyana cewa ba zai yiwu a sake ba Atiku Abubakar takara ba a 2027 saboda ya saɓa doka.

Sanata Ned Nwoko ya ce APC a ƙarƙashin Tinubu za ta ƙirƙiri Jihar Anioma, maganar da Ganduje ya gasgata yana mai cewa shugaban kasa ya goyi bayan kudurin.
Siyasar Najeriya
Samu kari