Siyasar Najeriya
Daga sanar da ficewarsa daga NNPP zuwa ADC, jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso ya jawo wa jam'iyyar hadaka karin farin ji a wurin yan Najeriya.
Wani mutumi a Dutse da ke jihar Jigawa ya fasa aurar da ‘yarsa ana saura kwana daya saboda goyon bayan saurayin ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na Najeriya.
Hukumar INEC ta sanar da shirin fara tantance masu zabe yayin da ake maganar 2027. Mutane za su je ofisoshinta ko ta yanar gizo domin a tantance su.
Wata kungiyar matasa mai goyon bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta koka kan lalata allon tallata shugaban kasar a Akure, jihar Ondo kan zaben 2027.
Ministar kwadago, Nkeiruka Onyejeocha, ta yi murabus daga gwamnatin Tinubu a yau Juma'a, inda ta bayyana hakan a matsayin bude sabon babi na hidimar kasa.
Jam’iyyar APC ta musanta rahoton cewa za ta bai wa gwamnoni da ‘yan majalisa tikitin kai tsaye, tana jaddada cewa dole kowa ya shiga zaben fidda gwani.
'Yan siyasa da suka hada da nasiru Yusuf Gawuna, Aminu Abdulsalam Gwarzo, Yaya Bauchi Tongo da sauransu sun shiga ADC bayan sauya shekar Rabiu Musa Kwankwaso.
Jam'iyyar NNPP mai adawa ta tausayawa takwararta ta ADC kan rikicin da take fama da shi. Jam'iyyar NNPP ta nuna yatsa ga Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
Jarumin fim, Musa Mai Sana'a ya bayyana cewa yana halin lafiya bayan rade-radin cewa an masa dukan tsiya kan tallata shugaba Bola Ahmed Tinubu a jihar Kano.
Siyasar Najeriya
Samu kari