Siyasar Arewa
Sheikh Bashir Ahmad Sani Sokoto ya sanar da cewa jam'iyyar ADC bata ba shi takara ba. Hakan ya nuna cewa ba zai yi wa jam'iyyar takarar gwamna ba.
Mai neman takarar gwamna a Taraba a karkashin jam'iyyar APC, David Sabo Kente ya ce dole a yi adalci ko jam'iyyar ta rushe a zaben 2027 da ke tafe.
Tsohon minista a Najeriya, Femi Fani-Kayode ya nuna goyon baya ga Sheikh Isa Ali Pantami yayin da ake shirin zaben fitar da gwani na jam'iyyar APC a Gombe.
Jam'iyyar APC ta kifar da mutum 150 a wajen tantance masu neman takarar 2027. Wasu 'yan jam'iyyar sun sauya sheka, wasu sun yi barazanar zuwa kotu.
Sheikh Isa Ali Pantami ya bayyana wasu abubuwan da suka bambanta shi da masu neman takarar jam'iyyar APC a jihar Gombe. Ya ce yana da kwarewa a fannoni daban-daban.
Surukin Sanata Danjuma Goje, Ibrahim Dasuki Waziri, ya bayyana goyon bayansa ga Gwamna Inuwa Yahaya duk da rikicin siyasar APC da ke kara zafi a Gombe.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa sun taimaki Muhammadu Buhari da kuri'u masu yawa amma ba su ci ribar komai ba har ya kammala mulki a 2023.
Kungiyar Arewa Youth Assembly ta yi zargin cewa ana wani shiri domin haddasa rikici a APC domin hana Bola Tinubu tazarce a zaben shekarar 2027 da ke tafe.
Gwamnan Kaduna, Uba Sani ya bayyana cewa 'yan adawa ba su kawo mafita ga halin da ake ciki a Najeriya ba, ya ce 'yan Arewa za su sake zaben shugaba Tinubu a 2027.
Siyasar Arewa
Samu kari