
Siyasar Arewa







Yayin da ake tsaka da rikicin jam'iyyar PDP ta kasa, wasu daruruwan mambobinta sun watsar da ita inda suka koma jam'iyyar APC mai mulki a jihar Nasarawa.

Kusa a PDP, Dele Momodu ya dura kan masu sukar takarar Atiku Abubakar takara a zaben 2027.Momodu ya ce Tinubu ya kamata a fara hanawa takara a 2027.

Tsagin NNPP a Najeriya ya bukaci Sanata Rabi'u Kwankwaso ya ajiye jagorancin jam'iyyar a Najeriya. Haka zalika tsagin ya bukaci a ladabtar da Abba Kabir Yusuf.

Farfesa Abubakar Sani Lugga ya yi magana kan kiraye-kirayen da yan Kudu ke yi game da raba Najeriya inda ya ce ya kamata yan Arewa su shirya zama bayan rabuwa.

Akwai ‘yan gidan Olusegun Obasanjo da Bola Tinubu da ke siyasa. Rabiu Kwankwaso ya bi sahun Yar’adua, Saraki, Ibrahim Waziri domin akwai ‘yan siyasa a cikin jininsa

Sanata Shehu Buba Umar mai wakiltar Bauchi ta Kudu ya ce lokacin fara tattaunawa kan yakin neman zabe bai yi ba amma ya kusa amsa kiran fitowa takarar gwamna.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Filato (PSIEC) ta fara sanar da sakamakon zaben kananan hukumomin jihar inda ta ce PDP ta lashe kujeru 10 zuwa yanzu.

Kungiyar ACF ta bayyana cewa sun fara daukar matakan da za su magance karuwar rashin tsaro da rarrabuwar kai tsakanin mazauna Arewacin kasar nan.

Yayin da ake shirye-shiryen zaben 2027, Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya shawarci jiga-jigan APC su hada kai wurin samun nasara a zaben kananan hukumomi.
Siyasar Arewa
Samu kari