Siyasar Arewa
Jam'iyyar PDP ta sanar da cewa ba za ta sanya 'yan takara a zaben kananan hukumomin jihar Borno da za a gudanar ranar Asabar ba, saboda wasu dalilai.
Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya bayyana cewa ba shi da wani shiri na barin PDP, ya kuma soki jam'iyyar PRP da cewa ba zai bari kage ya dauke masa hankali ba.
Tsohon ministan kwadago Joel Danlami Ikenya ya fice daga jam’iyyar APC ya koma PDP, yana mai cewa matakin ya biyo bayan bukatar al’umma da makomar siyasar Taraba.
Jam'iyyar PRP ta bayyana cewa ba ta da wurin da za ta karbi Gwamna Bala Mohammed ko da rahoton da ake yadawa gaskiya ne, ta ce ya illata jihar Bauchi.
Gwamna Caleb Mutfwang na shirin barin PDP ya koma jam'iyyar APC kafin ƙarshen Janairu 2026, duk da adawa daga wasu manyan jiga-jigan APC a jihar Plateau.
Tsohon shugaban APC, Abdullahi Umar Ganduje ya ce lokaci bai yi ba da za a fara tallata dan takarar gwamna karkashin APC a Kano bayan fara tallata Barau.
Jam'iyyar APC ta sanar da cewa ba za a gudanar da taron shigar Gwamna Kefas Agbu jam'iyyar a 2025 ba. APC ta ce za a yi taron ne a Janairun 2026.
Kungiyar Arewa Youth Consultative Forum ta ce makomar Tinubu a 2027 za ta dogara kan yadda gwamnatinsa ta shawo kan tsaro da matsin tattalin arziki.
A labarin nan, za a ji Mawaki Dauda Kahutu Rarara ya ce dole mutum ya rika tuna tushensa tare da yin aikin alheri domin gode wa ni'imar da Allah SWT ya yi masa.
Siyasar Arewa
Samu kari