
Jihar Rivers







Kungiyar SERAP ta dauki matakin shari'a kan dakatarwar da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Gwamna Siminalayi Fubara da 'yan majalisar dokokin Rivers.

Karamin ministan gidaje da ci gaban birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya taso Rabiu Musa Kwankwaso a gaba kan kalaman da ya yi dangane da dokar ta baci a Rivers.

Mai magana da yawun APC na ƙasa, Felix Morka ya caccaki mulkin dakataccen gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce Tinubu ya yi haka ne domin dawo da soka.

Majalisar wakilai ta fito ta yi magana kan zargin da aka jefe ta da shi na karbar cin hanci kafin amincewa da bukatar Shugaba Bola Tinubu kan dokar ta baci a Rivers.

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya yi magana kan matakin da Shugaba Bola Tinubu ya dauka na dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara na Rivers.

Shugaban rikon kwarya a jihar Rivers, Vice Admiral, Ibok-Ete Ibas ya umarci a biya ma’aikatan kananan hukumomi albashin da suke bi ba tare da bata lokaci ba.

Dan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Yusuf Shittu Galambi, ya musanta zargin da ake jifan 'yan majalisa da shi na karbar cin hanci kan dokar ta baci a Rivers.

A makon da ya gabata, tsohon gwamnan Ribas kuma Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya samu nasarori da dama, wadanda za su girgiza jam'iyyarsa ta PDP.

Kungiyar gwamnonin Najeriya ta yi magana kan dakatar da gwamna Siminalayi Fubara da Bola Tinubu ya yi a makon da ya wuce. Sun fadi dalilin yin shiru kan lamarin.
Jihar Rivers
Samu kari