Jam'iyyar PDP
Sanatocin Taraba, Haruna Manu da Shuaibu Isa Lau, sun fice daga PDP zuwa APC yau 4 ga Fabrairu, 2026. APC ta mamaye majalisa da kujeru 81 yayin da PDP ke durƙushewa.
Wani dan majalisar wakilai daga jihar Adamawa, Muhammad Basil, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya ja baya da siyasa.
Tsohon gwamnan Benue, Gabriel Suswam, ya fice daga PDP, yana zargin rashin haɗin kai da rikice-rikicen cikin gida da suka tilasta masa yin murabus.
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya yi yunkurin jawo gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri zuwa jam'iyyar APC. Sai dai, Bukola Saraki, ya yi masa martani.
Jam'iyyar hadakar yan adawa watau ADC ta kara karfi a jihar Kuros Riba bayan ahigar tsohon gwamna, Donald Duke, wanda ya karbi katin zama cikakken mamba.
Wata babbar kotun jihar Oyo da ke birnin Ibadan ta soke babban taron PDP da aka gudanar. Kotun ta hana shugabannin da aka zaba ayyana kansu a matsayin shugabanni.
Fasto Abel Boma ya bayyana cewa Seyi Makinde zai gaji Bola Tinubu a matsayin shugaban ƙasa, yana jaddada cewa Allah ya shirya masa hanya zuwa ga jagoranci.
Bolaji Abdullahi ya ce tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya cire shi daga mukamin minista saboda ya ki sukar Bukola Saraki a yakin neman zabe.
Bayan Gwamna Abba Yusuf ya koma APC; jam’iyyar PDP ta tsira da gwamnoni 4 kacal yayin da siyasar 2027 ke daukar sabon bayan sauya shekar manyan gwamnoni.
Jam'iyyar PDP
Samu kari