Jihar Oyo
Wasu tsofaffin Ministocin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu sun rasa tikitin takara a jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya bayan sun yi murabus daga gwamnati.
Gwamnatin jihar Oyo ta fara rabon kayan abinci masu rangwame ga ma’aikata kafin Babbar Sallah, inda ta kashe sama da Naira miliyan 120 kan shinkafa, mai da raguna.
Jam'iyyar APC ta gudanar da zaben fitar da gwani domin zabar dan takarar gwamna a jihar Oyo. Sanata Sharafadeen Alli ya laasa tsohon Minista, Bayo Adelabu.
Da safiya yau Juma'a, wasu yan bindiga suka kutsa makarantar sakandire a jihar Oyo, inda suka sace shugabar makarantar da dalibai da yawa da ba a tantance ba.
Rundunar 'yan sanda ta cafke wani mai garkuwa da mutane bayan ya yi yunkurin karbar kudin fansa N10m a jihar Oyo. Masu garkuwar sun sace wani mutum a gidan shi.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya nuna cewa gwamnan Oyo da ya fito takara a 2027 ba zai yi nasara ba. Ya bayyana cewa bai yarda da wata hadaka tsakanin PDP da APM ba.
Wasu magoya bayan jam'iyyar APC sun yi zanga-zangar adawa da kakaba 'yan takara da suka ce an yi kafin zaben fitar da gwani. Sun yi fashe-fashe a zanga-zangar.
Tsohon Minista Adebayo Adelabu ya ayyana takarar gwamnan Oyo a 2027 karkashin APC ranar 12 ga Mayu, 2026, tare da kaddamar da shirin "Oyo Rebirth Agenda."
Gwamna Seyi Makinde zai kaddamar da takarar shugabancin kasa a 2027 tare da kawancen PDP-APM a dandalin Mapo Hall, Ibadan ranar 14 ga Mayu, 2026.
Jihar Oyo
Samu kari