Nyesom Wike
Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara ya roki Ministan Abuja kuma tsohon uban gidansa, Nyesom Wike kan samuwar zaman lafiya a jihar, amma ya ce hakansa bai cimma ruwa ba.
Gwamna Siminalayi Fubara ya nuna damuwa kan martanin da Shugaba Bola Tinubu ya yi game da rikicin jihar Rivers inda shugaban ya kira sunansa shi kadai.
Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya roki Ministan Abuja, Nyesom Wike da ya bar rigimar jihar ta wuce inda ya ce bai kamata rikicin ya ruguza cigaban jihar ba.
Karamar jam'iyya ta APP ta lashe zabe a kananan hukumomin Rivers yayin da PDP da APC suka fadi. Rikicin Fubara da Wike na cikin abubuwan da suka jawo nasarar APP.
Bola Ahmed Tinubu ya ba yan sanda umarni kan rikicin bayan zabe da ya tsananta a RIvers. Tinubu ya bukaci yan sanda su dakatar da kone kone da dawo da zaman lafiya.
Rahotanni sun ce 'yan bindiga sun fatattaki ciyaman a lokacin da suka kai farmaki sakatariyar karamar hukumar Ikwere da ke jihar Ribas a ranar Litinin.
Gwamna Sim Fubara na jihar Ribas, a yau (Lahadi) zai rantsar da sababbin zababbun shugabannin kananan hukumomin jihar. An ce za a yi rantsarwar da karfe 4.
Rahotanni sun bayyana cewa jam'iyyar APP da Gwamna Siminalayi Fubara ya tura mutanensa su yi takara a ciki ta lashe kujeru 22 cikin 23 na kananan hukumomin Ribas.
Fitaccen dan gwagwarmaya a yankin Neja Delta, Asari Dokubo ya gargadi rundunar sojoji da yan sanda a jihar Rivers bayan ganin jirgi na shawagi a saman gidansa.
Nyesom Wike
Samu kari