Jami'o'in Najeriya
Gwamnan jihar Katsina ya ba dalibin da ya gama jami'a da daraja ta daya ya fara tallan ruwa aiki aiki. Dalibin mai suna Sham'unu Ishaq ya gama jami'a a Katsina.
Kwamitin gudanarwa na Jami’ar Lokoja, karkashin Victor Ndoma-Egba, ya kori malamai hudu kan zargin lalata da dalibai, yana jaddada muhimmancin ladabi a jami’a.
Shugaba Tinubu ya yi kira ga matasa su amfani da iliminsu wajen kawo ci gaba a Najeriya, su guji neman dama waje. Ya ce gwamnati ta zuba jari mai yawa a iliminsu.
Jami'ar tarayya da ke Dustin-ma ta karrama Godswill Akpabio, matar Tinubu da Aliyu Magatakarda Wammako da digirin digirgir na girmamawa a Arewacin Najeriya.
Gwamnatin tarayya ta fara biyan ma'aikatan jami'o'i albashin da suke bi tare da biyan waɗanda suka yi ritaya hakkinsu, hakan na zuwa bayan NASU ta shiga yajin aiki.
Gwamnatin tarayya da gamayyar kungiyar ma'aikatan Najeriya sun gaza cimma matsaya domin kawo karshen yajin aikin da ake yi saboda hana su albashin wata 4.
Gwamnan jihar Abia, Alex Otti ya sallami shugaban jami'ar ABSU da ke garin Uturu tare da mataimakansa daga aiki, ya naɗa waɗanda za su maye gurbinsu.
Kungiyar malaman jami'o'i ta kasa (ASUU) a jami'ar jihar Gombe ta janye yajin aikin da ta shiga. Ɗaliban jami'ar Gombe za su koma makaranta bayan yajin aiki.
Wani hazikin matashi, Ayodeji Akinsanya ya kammala karatun digiri a fannin lissafi da maki 4.97, ya kafa tarihi a jami'ar Ilorin da ke jihar Kwara.
Jami'o'in Najeriya
Samu kari