
Jami'o'in Najeriya







Jami’ar OAU ta shiga alhini bayan Farfesa Jimoh Olanipekun ya yanke jiki ya fadi ana taro. An gaggauta kai shi asibiti, amma daga bisani aka tabbatar da rasuwarsa.

Jami'ar Maiduguri ta rage lokacin aiki ga dalibai da malamai saboda fara azumin watan Ramadan na 2025 domin samun damar yin ibada yadda ya kamata.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sababbin jami'o'i 11 masu zaman kansu a faɗin Najeriya, ministan ilimi ya ce hakan zai ƙara ba matasa dama.

‘Yan bindiga sun sace dalibai hudu a jami'ar FUDMA da ke jihar Katsina, yayin da aka ce wasu mahara sun kashe mutane 10 a wurin hakar ma’adinai a Neja,

Kungiyar ASUU reshen Jami’ar Sokoto ta fara yajin aiki na dindindin saboda rashin biyan albashi da alawus, tana zargin gwamnati da nuna halin ko-in-kula.

Wasu miyagun ƴan bindiga sun kai farmaki kan ɗaliban da suka fito karatu a jami'ar tarayya da ke Makurɗi a jihar Benuwai, sun yi awon gaba da mutum huɗu

'Yan sanda sun hallaka wani matashin dalibi da suke zargin yana da hannu a kai wa 'yan ta'adda bayanan sirri a wasu yankunan jihar Katsina da ke Arewa masu Yamma.

Tinubu ya amince da sabbin jami’o’i a Ekiti da Osun don inganta noma, fasaha da muhalli, tare da bunkasa tattalin arziki da kirkire-kirkire a Najeriya.

Jami'ar Tarayya da ke Lokoja a jihar Kogi ta bayyana alhininta bisa mutuwar ɗalibanta biyar a wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da su, ta dakatar da karatu.
Jami'o'in Najeriya
Samu kari