Hukumar Sojin Najeriya
Hafsan tsaron Najeriya, Janar Oluyede ya sanar da cewa za a tura dakaru na musamman zuwa Kwara da Niger. Ya nemi a ƙarfafa ƴan sanda da jami'an NSCDC.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta sha alwashin cewa duk mai hannu a harin da aka kashe daruruwan musulmi a jihar Kwara zai fuskanci hukunci daidai da abinda ya aikata.
Rundunar yan sanda reshen jihar Zamfara ta tabbatar da cewa an gano wani bam da yan ta'adda suka dasa a kan titi a Tsafe, jami'an tsaro sun warware shi.
Bayan tabbatar da an yi yunkurin juyin mulki a Najeriya, aka fara bankado bayanan abubuwan da bincike ya gano game da shirye-shiryen da masu hannu a lamarin suka yi.
Manjo Janar Ijioma mai ritaya ya bukaci yan Najeriya da kada su yi tunanin sojojin Amurka za su fito filim yaki su tunkari yan bindiga, ya ce ba haka abin yake ba.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta kore fargabar da mutane ke yi kan illar turo sojojin Amurka, ta ce hakan ba zai taba yancin kasar ba kuma komai an yi shi bisa tsari.
'Yan bindiga sun kashe soja 1 da farar hula 5 a Zurak, Jihar Filato; mutane na tserewa daga Wase zuwa Kampani sakamakon tsoro da fargabar wasu karin hare-hare.
Bayanai daga mazauna yankunan da yan bindiga suka kai hari a Kwara na nuna cewa adadin mutanen da suka rasa rayukansu ya tunkari 100, an ce an tura jami'an tsaro.
Babban lauya mai fafutukar kare hakkin dan adam, Femi Falana ya yi fatali da shirin gurfanar da jami'an da ke da hannu a kitsa juyin mulki a gaban kotun soja.
Hukumar Sojin Najeriya
Samu kari