Labaran tattalin arzikin Najeriya
Ministan sufuri, Sanata Said Alkali ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ya umarci Kashim Shettima ya gana da shugaban kasar China domin neman tallafin kudi.
Babban bankin Najeriya CBN ya bayyana cewa yana shirin rage kudin ruwa domin daidaita lamura a kasa. Mataimakin gwamnan bankin, Philip Ikeazor ne ya bayyana haka.
Shugaban sojin ruwan Najeriya ya ce maganin matsalar tsaro a Najeriya ba komai bane face 'yan Najeriya su koma ga Allah su dukufa da addu'a gadan-gadan.
Rahotanni sun bayyana cewa gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya kulla yarjejeniya da hukumar SMEDAN domin ba kananun 'yan kasuwar Katsina tallafin N1bn.
Mai shari’a Deinde Isaac Dipeolu na babbar kotun tarayya ya umarci tsohuwar ministar harkokin jin kai da ta yi bayanin N729bn da ta ce an rabawa talakawan Najeriya.
Gwamnatin tarayya ta tsawaita wa'adin masu sana'ar PoS na yin rijista da hukumar kula da kamfanoni, CAC, zuwa ranar 5 ga watan Satumbar 2024 domin 'yan karkara.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa abin kunya ne a ce kasar nan har yanzu tana samar da 4.5GW ne kawai na wutar lantarki duk girmanta.
Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya bayyana tsawon lokacin da zai dauka wajen dawo da tattalin arzikin Najeriya cikin hayyacinsa.
Bola Tinubu ya rantsar da majalisar tattalin arzikin shugaban kasa (PECC) wadda ta kunshi jami'an gwamnati, 'yan kasuwa da mashawarta ciki har da Aliko Dangote.
Labaran tattalin arzikin Najeriya
Samu kari