Labaran tattalin arzikin Najeriya
Masu shigo da kaya sun fara maganar karin farashin kayan masarufi yayin da kamfanin jigilar kaya na MSC ya kara kudin shigo da kwantena daga kasar waje.
Hasashe ya nuna 'yan Najeriya miliyan 141 za su rayu cikin talauci a 2026; fadar shugaban ƙasa ta yi watsi da waɗannan alƙaluma, tare da fadin matakan da aka dauka.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa za a ba talakawa miliyan 10 tallafin a 2026. Za a ba mutum 1,000 a dukkan mazabu 8,809 tallafin a Najeriya.
Sabuwar hukumar tattara haraji ta Najeriya watau NRS ta fara aiki bayan shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu, an fitar da tambarin hukumar.
Ƙungiyar ɗalibai ta NANS ta ayyana 14 ga Janairu, 2026 a matsayin ranar zanga-zangar ƙasa kan sabuwar dokar haraji, tana mai kiran ɗalibai su yi tattaki zuwa Villa.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da tabbaci kan lokacin fara aiwatar da sabuwar dokar haraji. Ya ce ba gudu ba ja da baya kan lokacin da aka tsara.
Gwamnonin jihohin Lagos, Abia, Ogun, Enugu, Osun, Delta, Sokoto, Edo, Bayelsa da Gombena shirin ciwo bashin Naira tiriliyan 4.287 a 2026 kan kasafin kudi.
Daga 1 ga Janairun shekarar 2026, bankuna za su fara cire ₦50 harajin hatimi (stamp duty) kan duk wata tura kuɗi ta lantarki daga ₦10,000 zuwa sama.
Cikin abubuwan da za su faru a 2026, Aliko Dangote zai fara raba mai kyauta, dokar haraji, cire kudi za su fara aiki, za a yi zabe a Ekiti da Osun, APC za ta yi taro
Labaran tattalin arzikin Najeriya
Samu kari