Labaran tattalin arzikin Najeriya
Naira ta shiga sabon mako da ƙarfinta, inda ake cinikinta kan N1353.54/1$ a kasuwar NFEM yau 16 ga Fabrairu, 2026. Farashin kasuwar bayan fage ya kai N1420/1$.
Farashin kayan abinci ya kara sauka sosai a kasuwannin jihar Taraba yayin da al'ummar Musulmi ke kara shirin wata Ramadan. Yan kasuwa sun yi korafi kan hakan.
Hukumar NISO mai kula da wutar lantarki ta kasa ta ce ana fargabar rage samun wutar lantarki a Najeriya yayin da za a yi gyara a wasu cibiyoyin iskar gas.
Gwamna Inuwa Yahaya ya kulla yarjejeniyar zuba jari da tawagar TUCAD ta ƙasar Tunisia kan wasu muhimman fannoni, ciki har da ruwa, makamashi da sufuri a Jihar Gombe.
Matatar Dangote ta sanar da rage kudin litar man fetur daga N799 zuwa N774. An samu saukin N25 a halin yanzu. Dangote ya je kasar Burundi domin zuba jarin kasuwanci.
Gwamnatin tarayya ta ki amincewa da neman dakatar da hako ma'adanai a Arewa na wata shida da gwamnonin Arewa suka nema a yi kan rashin tsaro a yankin.
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya wakilci shugaba Bola Tinubu wajen kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin mata miliyan 25 a Najeriya.
Bankin Duniya ya tabbatar da cewa sauye-sauyen tattalin arzikin Najeriya da Shugaba Tinubu ya yi sun zama abin misali domin a tattaunawa a kansu a matakin duniya.
A labarin nan, za a ji cewa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce duk da ana jin jiki a kan manufofinsa, ba za a janye su na saboda suna haifar da ɗa mai ido.
Labaran tattalin arzikin Najeriya
Samu kari