Hukumar yan sandan NAjeriya
Rundunar yan sanda da rundunar sojojin Najeriya sun karyata labarin da ke yawo cewa an khe jami'an sojoji 21 a jihar Anambra, sun ce IPOB ce ke yaɗa farfaganda.
Wani malamin addinin musulunci ya bankawa gidan matarsa wuta a jihar Ekiti saboda ta ki yarda su yi Sallar dare. Jami'an 'yan sanda sun kama shi.
Miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun salwantar da ran wani kwamandan rundunar NSCDC a jihar Benue. An hallaka 'yan bindiga da dama yayin artabun.
Wasu miyagun ƴan bindiga sun kai farmaki kan makarantar sakandire a kauyen Adeke da ke jihar Benuwai ranar Talata da daddare, sun jikkata mai gadi ɗaya.
Wasu gungun 'yan banga sun yi ajalin wani babban jami'in ɗan sanda, ASP Tapu Godfrey a kauyen Sardauna da ke karamar hukumar Gassol a jihar Taraba.
Yan sanda da taimakon jami'an DSS sun yi nasarar kama haramtattun ƴan canji 17 a kasuwar hada-hadar musayar kuɗi ta Wapa da ke yankin Fagge a jihar Kano.
Yan sandan jihar Ogun sun sanar da kashe masu garkuwa da mutane biyu tare da kwato kudin fansa naira miliyan 7.9. Sun kuma sanar da cewa suna kokarin kamo sauran.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun aikata sabon ta'addanci a jihar Zamfara bayan sum hallaka mutum takwas tare da sace manajan banki a wasu hare-hare.
Wasu ƴan fashin teku sun tare jirgin ruwa mai ɗauke da mutum 20 a kogin Onne ranar Litinin, sun yi masu tatas kana suka yi awon gaba da mutum bakwai ranar Litinin.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari