
Rashawa a Najeriya







Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta bayyana cewa wasu tsofaffin shugabannin hukumar tattara kudin haraji a jihar sun yi sama da fadi da hakkokin jama'a.

Tsohon dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar ya nemi gwamnatin APC ta tabbatar da cewa ta bayyana yadda ake kashe kudin da aka ware wa fannin lafiya.

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan kwangilolin bogi da suka lakume Naira biliyan 167, inda ta bukaci a gurfanar da 'yan kwangilar don dawo da dukiyar gwamnati.

Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El Rufa'i ya yi zargin gwamnati mai ci a jiharsa da siyasantar da binciken rashawa da ake yi wa wasu daga cikin jami'an gwamnatinsa.

Tsofaffin jami'an gwamnatin jihar Kaduna sun zargi gwamna mai ci, Uba Sani da kokarin bata wanda ya gada a idon Najeriya ta hanyar manna masa rashawa.

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i ya ce maganar Hajiya Na'atu ta yi a kan Bola Tinubu game da rashawa gaskiya ne. Ya fito da hujjoji kan zargin Tinubu.

Kungiyar dattawan jihar Katsina ta bukaci Bola Tinubu ya saki tsohon shugaban NHIS, Farfesa Usman Yusuf da EFCC ta kama. Sun ce kawai saboda yana sukarsa ne

Shugaban jami'ar tarayya ta Gusau, Farfesa Muazu Abubakar, ya fito da bayanai a kan zargin cewa 'yan majalisa sun nemi shugabannin jami'o'i su bayar da cin hanci.

Kotun Kano ta hana kama Muhuyi Magaji Rimingado, yayin da 'yan sanda suka fayyace cewa ba kama shi suka yi ba, an gayyace shi ne kawai domin bincike.
Rashawa a Najeriya
Samu kari