Musulmai
A labarin nan, za a ji mabiya Ƙadiriyya a Kano sun yi wa jagoran addini na Iran, Ayatollah Khamenei sallatul gha'ib bayan harin Amurka da Isra'ila ya yi ajalinsa.
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun shiga wani masallaci sun yi harbi da bindiga ana sallar tarawihi. 'Yan ta'addan sun sace maza da mata 6 a masallacin.
Kasar Saudiyya ta sanar da cewa ta tare makaman roka na Iran da aka harba domin kai hari filin jirgin Riyadh da sansanin Prince Sultan wanda ya tayar da hankali.
Hukumomi a Amurka sun tabbatar da cewa wasu sojojin kasar uku sun mutu a hare-haren Iran, biyar sun jikkata, sai dai an musanta jita-jitar hari kan Abraham Lincoln.
Sakon bogi ya yi ikirarin cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya mutu a harin jirgi mara matuki, amma binciken gaskiya ya tabbatar da cewa na raye.
Malamin addinin musulunci, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana jagoran Iran da aka kashe, Imam Khamenei a matsayin mai sa'a, wanda ya rasu wajen kare gajiyayyu.
Dubban mutane sun taru a Tehran don makokin Ayatollah Ali Khamenei, yayin da IRGC ta yi alkawarin ramuwar gayya kan Isra’ila da Amurka a yankin Gulf.
Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman tattauna da Donald Trump akan rikicin Gabas ta Tsakiya da goyon bayan Amurka ga kasar bayan harin makamai daga Iran.
Mutum hudu sun rasa rayukansu yayin da 18 suka jikkata a rabon Zakkar da aka yi a Ramadan a Katsina, jami'an 'yan sanda na gudanar da bincike kan lamarin.
Musulmai
Samu kari