Masu Garkuwa Da Mutane
Gwamnatin jihar Kebbi ta sanar da cewa adadin dalibai mata da 'yan bindiga suka sace a makarantar GCGSS Maga ya haura 25, sabanin rahotannin da ake yadawa.
Wasu daga cikin iyayen dalibai mata da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a Kebbi sun mamaye harabar makarantar. Wata mahaifiya ta ce ba za ta koma ba.
Dan majalisar Amurka, Riley Moore ya ce ya san a yankin Kiristoci aka sace daliban GGSSC Maga a jihar Kebbi. Bashir Ahmad ya masa martani kan kuskuren da ya yi.
Shaidun gani da ido sun fadi yadda aka sace daliban makarantar GGCSS Maga da asuba a jihar Kebbi. Yan bindiga sun harbe mataimakin shugaban makarantar.
Shugaban sojojin kasan Najeriya, Laftanar Janar Waidi Shuaibu ya ziyarci jihar Kebbi bayan sace daliban makarantar GGCSS Maga da aka sace. Ya ce za a ceto su.
'Yan bindiga dauke da miyagun makamai sun kai hari makarantar kwana, inda suka kashe mataimakin shugaba, suka sace dalibai masu yawan gaske a jihar Kebbi,
Rahotanni daga jihar Kwara sun nuna cewa yan bindiga sun yi garkuwa da Alhaji Abubakar Sise, dan kasuwa kuma tsohon shugaban PDP a mazabar Boriya–Shiya.
‘Yan bindiga sun tare fasinjoji a hanyar Ayere–Kabba, jihar Kogi, inda suka kashe mutum ɗaya, suka sace wasu, yayin da gwamnati ke cewa tsaro ya inganta da 81%.
‘Yan gida daya su 2 da aka sace a Imoga, jihar Edo, sun tsero bayan masu garkuwar su sun yi bacci a daji, yayin da aka nemi gwamnati ta kafa ofishin ‘yan sanda.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari