Masu Garkuwa Da Mutane
Gwamnatin Katsina ta ce an dade da dakatar da Nura Garwa daga mukaminsa na hadimin Gwamna Dikko Radda, ana zarginsa da alaka da wata kungiyar masu garkuwa.
Mohammed Hayatudeen na ADC ya yi alƙawarin ayyana ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane a matsayin ‘yan ta’adda idan ya zama shugaban Najeriya a 2027.
Da safiya yau Juma'a, wasu yan bindiga suka kutsa makarantar sakandire a jihar Oyo, inda suka sace shugabar makarantar da dalibai da yawa da ba a tantance ba.
Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin Tinubu kan mutuwar Hon. Abba Anas Adamu a hannun masu garkuwa ranar 12 ga Mayu, 2026, yana mai kiran a gyara tsaro da gaggawa.
Tsohon mamban majalisar wakilan tarayya, Hon Abba Anas Adamu ya rasa rayuwarsa a hannun 'yan bindiha duk da an biya kudin fansa Naira miliyan 50.
Sarkin da aka sace a jihar kogi, Adebayo Samuel ya rasu a cikin daji bayan kwanaki a hannun masu garkuwa da mutane. Mutane sun shiga jimami a garinsu.
Mazauna yankin a karamar hukumar Sabon Birni sun ce maharan sun shafe tsawon awanni suka cin karensu babu babbaka ba tare da kawo dauki ba a Sokoto.
'Yan bindiga sun kashe wani fasto tare da sace masu bauta da dama, ciki har da tsofaffi da yara, yayin wani taron addini a garin Eda Oniyo da ke jihar Ekiti.
Fiye da kauyuka 30 a Zamfara sun tsere daga gidajensu sakamakon janyewar dakarun tsaro daga kauyen Lilo, lamarin da ya bar su cikin fargabar harin 'yan bindiga.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari