Masu Garkuwa Da Mutane
Rundunar 'yan sandan jihar Kebbi ta gargadi masu shirya zanga zanga kan sace dalibai a GGCSS Maga a jihar Kebbi. Ta ce hakan zai dagula kokarin ceto daliban.
Ministan tsaro Bello Matawalle ya isa Birnin Kebbi domin aiwatar da umarnin Shugaba Tinubu na hanzarta ceto dalibai akalla 25 na GGCSS Maga da aka sace.
Rundunar ’yan sanda ta Nasarawa ta karyata rahotannin da ke nuna cewa an sace dalibai biyu a makarantar St Peter’s Academy, da ke jihar. Ta ce rahoton ƙarya ne.
An yada wasu rahotanni da ke cewa 'yan bindiga da suka sace mutane a wani coci a Kwara na neman kudin fansa har Naira biliyan 3 inji wani da ya ce an kira shi a waya
Gwamna Umaru Bago na jihar Neja ya yi magana kan sace dalibai da aka yi a jihar Neja. Gwamna Umaru Bago ya ce tun a karon farko an nemi a rufe makarantar.
Wasu 'yan bindiga masu garkuwa da mutane sun sace dalibai da malamai a wata makaranta a jihar Neja bayan sace wasu da dama a jihar Kebbi da kai hari Kwara.
Ƴan bindiga sun sake kai hari Kwara, inda a wannan karon suka farmaki manoma a kauyen Bokungi, tare da sace hudu daga ciki. Wannan na zuwa bayan harin coci.
Sanata Mai wakiltar Kebbi ta Kudu a Majalisar Dattawa, Garba Musa Maidoki ya ce yan bindigar da suka sace yan mata a makarantar Maga ba su bar mazabarsa ba.
Gwamnatin jihar Kebbi ta sanar da cewa adadin dalibai mata da 'yan bindiga suka sace a makarantar GCGSS Maga ya haura 25, sabanin rahotannin da ake yadawa.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari