Masu Garkuwa Da Mutane
'Yan bindiga dauke da miyagun makamai sun kai hari inda ake aikin gina titin Saadu-Kaiama-Kosubosu a karamar hukumar Ekiti, jihar Kwara, inda aka sace 'yan China 2.
Yan sandan babban binrin tarayya sun kashe ’yan bindiga uku, sun kama babban dan ta'adda, kuma sun dakile mugun shirin garkuwa da mutane a Abuja.
Sarki Ojibara na Bayagan da wasu mutane shida sun tsere daga hannun ‘yan bindiga bayan artabun da jami’an sa-kai suka yi da miyagun a wani dajin Kwara.
Rundunar Scorpion Squad da ke karkashin 'yan sanda ta kama masu garkuwa da mutane biyu a Zamfara, ta kwato motoci uku da makamai, bayan sahihin bayanan leken asiri.
Rundunar ‘yan sandan Kogi ta tabbatar da cewa 'yan bindiga sun sace mutane biyu yayin da mutum daya ya tsere a harin da suka kai kan hanyar Isanlu zuwa Idofin.
Rahotanni sun nuna cewa wasu hatsabiban 'yan bindiga sun sace sace mai martaba Ojibara na Bayagan, watau Oba Kamilu Salami, a safiyar ranar Asabar din nan.
Wasu ma'aurata da suka fada hannun maau garkuwa da mutane a jihar Edo sun roki yan Najeriya su taimaka su hada masu kudin fansa Naira miliyan 50.
Kungiyar Diocese ɗin Katolika ta Kontagora ta fitar da sunayen mutum 265 — malamai, ma’aikata, daliban sakandare da firamare — da har yanzu suke hannun ’yan bindiga.
Mai magana da yawun majalisar dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya bayyana cewa Majalisa ta aminta cewa gwamnati ba ta biya kudin fansar daliban Kebbi ba.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari