Masu Garkuwa Da Mutane
Jerry Gana ya ce 'yan bindiga na amfani da dalibai a matsayin garkuwa bayan barazanar Trump, yana kira ga gwamnati ta karo haɗin gwiwa da ƙasashen waje.
Yobe ta rufe dukkan makarantun kwana a matsayin matakin kare ɗalibai bayan karuwar garkuwa da su a jihohi kamar Kebbi da Neja. Jihohi da dama sun bi sahu.
‘Yan sanda sun ceto mata da yara 25 a Zamfara yayin da Ministan tsaro, Matawalle ya tabbatar da gano inda aka boye dalibai mata na Kebbi da aka sace.
Makarantar St Mary Papiri da ke jihar Neja ta fitar da bayani cewa adadin daliban da aka sace a harin 'yan bindiga ya kai 303 bayan an nemi dalibai 88 an rasa.
Rundunar 'yan sandan jihar Kebbi ta gargadi masu shirya zanga zanga kan sace dalibai a GGCSS Maga a jihar Kebbi. Ta ce hakan zai dagula kokarin ceto daliban.
Ministan tsaro Bello Matawalle ya isa Birnin Kebbi domin aiwatar da umarnin Shugaba Tinubu na hanzarta ceto dalibai akalla 25 na GGCSS Maga da aka sace.
Rundunar ’yan sanda ta Nasarawa ta karyata rahotannin da ke nuna cewa an sace dalibai biyu a makarantar St Peter’s Academy, da ke jihar. Ta ce rahoton ƙarya ne.
An yada wasu rahotanni da ke cewa 'yan bindiga da suka sace mutane a wani coci a Kwara na neman kudin fansa har Naira biliyan 3 inji wani da ya ce an kira shi a waya
Gwamna Umaru Bago na jihar Neja ya yi magana kan sace dalibai da aka yi a jihar Neja. Gwamna Umaru Bago ya ce tun a karon farko an nemi a rufe makarantar.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari