Masu Garkuwa Da Mutane
Kungiyar Diocese ɗin Katolika ta Kontagora ta fitar da sunayen mutum 265 — malamai, ma’aikata, daliban sakandare da firamare — da har yanzu suke hannun ’yan bindiga.
Mai magana da yawun majalisar dattawa, Sanata Yemi Adaramodu ya bayyana cewa Majalisa ta aminta cewa gwamnati ba ta biya kudin fansar daliban Kebbi ba.
'Yan bindiga dauke da miyagun makamai sun bude wuta kan mai uwa da wabi a Abuja, inda suka yi garkuwa da mata shida da kuma wani yaro dan shekara 16.
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari makarantar sakandare ta Kiri a Kogi, inda suka kashe mutum biyu, amma gwamnati ta tabbatar cewa ba a sace ɗalibi ko guda ɗaya ba.
Rundunar ’yan sandan Kwara ta tabbatar da sace mutane 10 a Isapa, tare da kaddamar da aikin ceto bayan harin da ake zargin makiyaya ne suka kai garin.
’Yan bindiga sun kai hari a Biresawa da wasu kauyuka a Tsanyawa, Kano, suka sace akalla mutum 8, ciki har da mata da matafiya. Mazauna sun tsere cikin dare.
Sojojin Najeriya sun kama wani babban mai garkuwa da mutane, Abubakar Bawa, a Wukari, yayin Operation Zafin Wuta da ke dakile aikace-aikacen miyagu a Taraba.
An rufe makarantu da dama da ke a kan iyakar Abuja da jihar Niger saboda matsalar tsaro bayan sace dalibai a Niger da Kebbi. Malamai sun ce matakin na kariya ne.
Kungiyar Katolika ta Kwantagora ta saki sunayen duka malamai da daliban sakandireda, firamare da nazire da yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Neja.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari