
Masu Garkuwa Da Mutane







Dakarun rundunar 'yan sanda sun ceto mata 5 a Kankara da wasu 2 a Malumfashi da ke jihar Katsina bayan fafatawa da ‘yan bindiga, an mayar da su gida lafiya lau.

Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya bukaci iyalan da mutanen da 'yan bindiga suka sace kan su daina biyan kudaden fansa.

Rahotanni sun tabbatar da cewa 'yan bindiga sun sace Blessing Adagba, mai taimakawa Gwamnan Ebonyi, a unguwar Okposhi Eheku da ke karamar hukumar Ohaukwu.

An miƙa Janar Tsiga da mutane 18 da aka ceto ga Nuhu Ribadu bayan ya shafe kwanaki 56 a hannun ‘yan bindiga. Ribadu ya yabawa jami’an tsaro kan wannan nasarar.

Bayan kwanaki 56 a hannun masu garkuwa, Janar Tsiga ya samu 'yanci. Iyalansa sun biya kuɗin fansa, amma an ci gaba da tsare shi na tsawon sati guda.

Wasu shugabannin 'yan bindiga a jihar Zamfara sun haukace bayan shan miyagun kwayoyi. Wasu na ganin zafafan addu'o'i da ake musu ne yasa suka haukace.

Dakarun Najeriya sun kashe Kachalla Dan Isuhu a jihar Zamfara. Dan Isuhu ya sa haraji a kauyuka 21, ya kashe Farfesa Yusuf na jami'ar Bayero, ya sace mutane da dama.

'Yan bindiga sun sace babban malamin addini, Rev. Fr. John Ubaechu a Imo. ’Yan sanda sun fara bincike, yayin da Kiristoci ke addu’a don kubutarsa.

‘Yan bindiga sun sace dalibai 2 a jami’ar FUDMA, da ke jihar Katsina yayin da aka ceto wani wanda aka yi garkuwa da shi a Adamawa, an kuma kama malami a Jigawa.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari