Manyan Labarai A Yau
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu daga cikin 'yan bindigan da suka kashe Sarkin Gobir. Sojojin sun sheke uku daga cikin miyagun har lahira.
Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a birnin Kano ta hana Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero daga yin gyara a fadar Sarkin da ke Nasarawa a cikin Kano.
Majalisar dokokin jihar Neja ta sanar da mutuwar daya daga cikin mambobinta. Mista Joseph Duza ya yi bankwana da duniya ne bayan ya yi gajeruwar jinya.
Wani ginin bene mai hawa uku ya rufto a kan daliban jami'ar Benin (UNIBEN). Ana fargabar dalibai da dama sun makale sakamakon ruftawar da ginin ya yi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yaba kan nasarorin da dakarun sojoji suka samu kan 'yan bindiga. Ya yaba kan kisan da aka yiwa Halilu Buzu Sububu.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa ya damu matuka kan yiwuwar wasu shugabannin 'yan Boko Haram sun tsere saboda ambaliyar ruwa.
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa matatar man Dangote za ta fira fitar da man fetur daga ranar Lahadi. Gwamnatin ta ce kamfanin NNPCL kadai za a ba fetur.
Tafiye tafiyen da uwargidan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, Remi Tinubu ta yi zuwa kasashen waje sun lakume kudade masu yawa. Gwamnati ta kashe N700m.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya sake fitowa ya nuna yatsa ga gwamnonin jam'iyyar PDP. Wike ya ce bai ci amanar jam'iyyar ba.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari