Manyan Labarai A Yau
A tarihin Najeriya akwai wasu manyan sojojin da aka taba yankewa hukunci kan yunkurin juyin mulki. Wasu daga cikin hukunce-hukuncen an aiwatar da su ta hanyar kisa.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a wani kauyen jihar Benue. Tsagerun sun hallaka jami'an tsaro na 'yan sanda tare da fararen hula yayin artabu.
Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya yi magana kan fitar da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC. Amaechi ya ba jam'iyyar ADC shawara.
Hukumar NiMet ta bayyana cikakken hasashen yanayin damina, karancin ruwa da farin da za a fuskanta a duka jihohin Najeriya a shekarar 2026,ta ja hankalin manima.
Majalisar dattawan Najeriya ta sauya matsayar da ta cimmawa da farko kan kin amincewa da tura sakamakon zabe ta yanar gizo. Ta amince da abu biyu.
Rahotanni sun nuna cewa gwamnan Bauchi, Bala Mohammed da takwaransa na jihar Oyo, Seyi Makinde sun halarci zaman kotun daukaka kara kan rigin shugabancin PDP.
Tsohon Ministan sufuri a gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari, ya halarci zanga-zangar neman gyara a dokar zabe a majalisar dattawa tare da dansa.
Wasu fusatattun matasa sun huce fushinsu kan wani dan majalisa a jihar Taraba. Dan majalisar ya tsallake rijiya da baya bayan farmaki ayayin motocinsa.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmed El-Rufai ya bayyana cewa bai taba zama abokin Shugaba Bola Tinubu ba. Ya yi magana kan dalilin sabanin da ke tsakaninsu.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari