Manyan Labarai A Yau
Matatar Dangote da ke jihar Legas ta rage farashin fetur zuwa N1,165 kan kowace lita daga N1,215, sannan ta sauke farashin dizal zuwa N1,570 a Najeriya.
Davido ya ce babu wanda zai iya kayar da shi a zaɓe mai gaskiya, amma ya ce rashin sahihancin tsarin zaɓen Najeriya ya hana shi shiga harkokin siyasa.
Fadar Sarkin Gombe ta karyata zargin cewa an hana Sarkin ganawa da Farfesa Isa Pantami, tana mai cewa labarin ƙarya ne kuma yana da alaƙa da siyasa.
Hukumomi sun cafke wani matashi a kusa da filin wasan Gulf na shugaban Amurka, Donald Trump, kwanaki kadan kafin ya kai ziyara, za a gurfanar da shi.
Sojojin Isra’ila biyu sun mutu, yayin da wasu bakwai suka jikkata bayan fashewar bam a wani gini da aka yi wa tarko a kudancin Lebanon a Gabas ta Tsakiya.
Gwamnatin Osun karkashin jagorancin Adeleke ta sake raba tallafin rage raɗaɗin tsadar rayuwa ga ma’aikatan gwamnati, domin ƙara musu albashi da inganta jin daɗinsu.
Farfesa Rabia Sa’id ta jami'ar BUK da ke Kano ta ce nadin da aka yi mata a kwamitin Majalisar Dinkin Duniya kan illolin yaƙin nukiliya ba sabon abu ba ne.
Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya kalubalanci shugaban EFCC kan daskare asusun jihar, yana zargin hukumar da ɗaukar matakin ba tare da umarnin kotu ba.
Sarkin Iwo, Oba Abdulrasheed Akanbi, ya haramta Hennessy da sauran giya a fadarsa, yana mai cewa barasa na iya jawo matsalolin lafiya ga dan Adam.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari