
Manyan Labarai A Yau







Kungiyar limamai da malamai sun bukaci gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ya yi gaggawar daukar matakan ceto al'umma kan tsadar rayuwa.

Gwamnatin jihar Yobe ta tuna da almajirai da ke karatu a makarantun Tsangaya. Ta raba musu kayayyaki domin su yi murnar zuwan lokacin bukukuwan Sallah.

Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya dakatar da shugaban rundunar tsaron jihar kan mummunan kisan gillar da aka yi wa mafarauta 'yan Arewa a jihar.

Mai alfama Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar, ya ta ya al'ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan. Ya ba da shawara kan shugabanni.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi magana kan dalilin da ya sa ya jawo Bosin Tijani ya ba shi mukamin ministan sadarwa duk da yana yawan sukarsa.

Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya taya al'ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan na shekarar 1446 bayan Hijira.

Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya goyi bayan matakin da jami'an tsaro suka dauka na hana gudanar da hawan Sallah a wannan shekarar.

Karamin ministan tsaron Najeriya, Bello Matawalle, ya yi rabon shanu ga mambobin jam'iyyar APC a jihar domin murnar bukukuwan karamar Sallah na 1446AH.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa a shekarar 2023, ya kusa hakura da yin takara, saboda yadda abubuwa suka cabe kan sauya fasalin Naira.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari