Manyan Labarai A Yau
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta samu koma baya a majalisar wakilan Najeriya. Wani dan majalisar wakilai daga jihar Gombe ya sauya sheka zuwa APC.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi martani kan batun ya cimma yarjejeniya da Gwamna Seyi Makinde don zama mataimakinsa a zaben 2027.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya ki yarda ya bi jami'an tsaro saboda babu wata takardar gayyata da aka turo masa a hukumance.
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gabatar da kasafin kudi don zaben shekarar 2027. INEC ta bayyana cewa hakan ya yi daidai da tanadin doka.
Mataimakin shugaban kasar Najeriya, Kashim Shettima, ya yi tafiya zuwa kasar Ethiopia. Shettima zai wakilci Mai girma Bola Tinubu a wajen taron kungiyar AU.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi sababbin zarge-zarge kan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Ya ce za su yo kokarin murde zaben 2027.
Alkali Obiora Egwuatu ya janye daga shari’ar tsohon Minista Abubakar Malami kan zargin N212bn a Abuja. Ya bayyana hakan ne a zaman kotu na yau 12 ga Fabrairu, 2026.
Nasir El-Rufai zai dawo Nijeriya nan da sa'o'i 48 domin amsa kiran EFCC a ranar 16 ga Fabrairu, 2026. Ya musanta zargin tserewa zuwa waje don gujewa masu bincike.
Tsohon hadimin shugaban kasa, Reno Omokri, ya goyi bayan Bola Tinubu a zaben 2027, yana jaddada amfanin manufofin gwamnatinsa ga talakan Najeriya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari