Manyan Labarai A Yau
Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya nuna goyon bayansa ga tazarcen shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027. Ya ce zai mara masa baya.
Jita-jitar komawar Gwamna Abba da Rabiu Kwankwaso zuwa APC na kara karfi, yayin da masana ke gargadin cewa matakin zai canza taswirar siyasar Kano kafin 2027.
Shugaban kungiyar Shi'a a Najeriya, Sheikh Ibrahim Zakzaky, ya yi zarge-zarge kan matsalar rashin tsaro. Ya nuna cewa gwamnati na da masaniya kan matsalar.
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya koka kan halin da 'yan siyasa ke nuna a Najeriya. Ya bayyana cewa sun dauki mukaman gwamnati daga su sai 'ya'yansu.
Tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmed Lawan, ya yi hasashe kan kuri'un da Mai girma Bola Tinubu zai samu a Arewacin Najeriya a zaben shekarar 2027.
Yan Majalisa sun kaure da hayaniya da muhawara mai zafi yayin da aka gabatar da wani kudirida ya nemi a gayyaci gwamnan babban bankin Najeriya (CBN).
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake tabo batun janye 'yan sanda daga gadin manya. Shugaba Tinubu ya nuna cewa ba gudu ba ja da baya kan umarnin da ya bayar.
Sanata mai wakiltar Bauchi ta Arewa, Abdul Ningi, ya koka kan janye masa jami'an 'yan sanda da aka yi. Ya nuna cewa umarnin ya kamata ya shafi kowa.
Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers ya bar PDP ya koma APC, inda ya shiga kara jerin gwamnonin da suka fice daga jam’iyyar tun bayan zaben 2023.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari