
Manyan Labarai A Yau







Gwamnatin Kano ta bullo da shirin yi wa 'yan daba afuwa. Ta bayyana cewa mutanen da za su amfana za a sake dawo da su cikin al'umma bayan an gyara musu tarbiyya.

Malamin addinin musulunci a jihar Sokoto, Sheikh Murtala Bello Asada, ya nuna rashin gamsuwarsa kan masu goyon bayan a yi sulhu da dan bindiga Bello Turji.

'Yan bindiga dauke da makamai sun kai hari kan wasu manoma a jihar Kaduna. Miyagun sun hallaka mutanen da ke dawowa daga gona bayan sun yi aikinsu.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya tabo batun matsalar rashin tsaro da ake fama da ita a Najeriya. Ya ce za a iya shawo kan matsalar gaba dayanta.

Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta tabbatar da rasuwar karamin Jakadan Najeriya a jamhuriyar Kamaru, Taofik Obasanjo Coker, ya mutu ranar Asabar.

Wani jigo a jam'iyyar APC a jihar Rivers, Eze Chukwuemeka Eze, ya yi wa Nyesom Wike martani mai zafi bayan ya nuna cewa Rotimi Amaechi, ba zai kai labari ba a 2027.

Gwamnati ta rufe asusun soshiyal midiya 13,597,057 na 'yan Najeriya, ta goge wallafe-wallafe sama da miliyan 58 saboda karya dokokin amfani da yanar gizo.

Gwamna Hyacinth Alia na Benue ya dakatar da shugabannin uku na gwamnati tsawon wata guda bisa shawarar majalisa, yana mai jaddada gaskiya, bin doka da riƙon amana.

Ministan harkokin cikin gida, Olabunmi Tunji-Ojo, ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai yi tazarce a zaben shekarar 2027 da ake tunkara.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari