
Kananan hukumomin Najeriya







Bayan gargadin gwamnatin Bola Tinubu kan sake zaben kananan hukumomi, Gwamna Ademola Adeleke ya dage cewa za a gudanar da zaben a Osun a gobe Asabar.

'Yan bindiga sun farmaki karamar hukumar Munya a jiahr Neja, sun sace sakataren karamar hukuma da wasu mutum huɗu. Jami’an tsaro sun fara bincike don ceto su.

Bayan hukuncin kotu da kuma rigimar da aka samu kan ikon kananan hukumomi, jam’iyyar APC ta janye daga zaben a Osun da aka shirya ranar 22 ga Fabrairun 2025.

Duk da rigimar da ta barke da aka rasa rayuka a Osun kan ikon ƙananan hukumomi, shugabannin APC na yankuna 14 da kansiloli a Osun sun koma ofisoshinsu.

Wasu rahotanni sun ce ana hasashen batan tsohon shugaban karamar hukumar Kalgo a jihar Kebbi, Umar Namashaya Diggi bayan wani mummunan harin yan bindiga.

Babbar kotun Kano ta tabbatar da ƴancin kananan hukumomin jihar 44, ta ba ɗa umarnin ci gaba da sakar masu kuɗaɗensu kai tsaye ba tare da wata tangarɗa ba.

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Katsina ta lashe zaben shugabannin kananan hukumomin da aka gudanar a jihar. APC ta lashe dukkanin kujerun gabadaya.

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya umarci shugabannin kananan hukumomi su fara biyan mafi karancin albashin N85,000 domin cika ka'idar aiki.

Shugaba Muhammadu Buhari ya ka da kuri'a a zaben kananan hukumomin jihar Katsina. Dandazon jama'a ne suka fito tarbar jama'a a lokacin da ya fito.
Kananan hukumomin Najeriya
Samu kari