Labarin Sojojin Najeriya
Tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom da Rivers a mulkin soja, Manjo-janar Godwin Osagie Abbe ya riga mu gidan gaskiya a jiya Asabar 21 ga watan Disambar 2024.
Sojoji sun kama 'yan tawaye 4 na Ambazonian a Taraba, sun kwace bututun man fetur 30. Rundunar ta yi kira ga jama’a su bayar da bayanai don tsaro.
Hukumomi a kasar Nijar sun zargi Najeriya da Bola Tinubu da neman kawo cikas a mulkin sojoji a kasar inda ta ce yana hada baki da wasu ƙasashen duniya.
Gwamnatin Katsina ta yabawa sojoji kan farmaki da suka kai kan gagga gaggan 'yan bindiga Manore da Lalbi a Bichi. Sojoji sun musu ruwan wuta ta sama da kasa.
Bako Wurgi, hatsabibin shugaban 'yan bindiga kuma na hannun daman Bello Turji, ya mutu sakamakon raunukan harbi, bayan ya ba sojoji bayanan sirri.
Bullar ƙungiyar Lakurawa a yankin Arewa maso Yamma na zama babban barazana ga shugabannin yan bindiga wanda ka iya zama tashin hankali tsakaninsu.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar cafke wasu mutane da ake zargi da jigilar makamai a jihar makamai. Sojojin sun kwato alburusai masu yawa.
Jami'an rusau a babban birnin tarayya Abuja sun gamu da sojoji.An yi zargin ma'aikatan Wike na shirin rushe ginin babban soja a lokacin da jami'an su ka isa wajen.
Dakarun sojoji na rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa (MNJTF) sun samu nasarar dakile wani hari da 'yan ta'addan Boko Haram suka kai a sansaninsu.
Labarin Sojojin Najeriya
Samu kari