Labarin Sojojin Najeriya
Harin da 'yan ta'addan Boko Haram suka kai kan sansanin sojoji a jihar Borno ya jawo asarar rayukan jami'an tsaro masu yawa. An nemi wasu daga ciki an rasa.
Rundunar soji ta 6 da ke sansani a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas ta yi nasarar muƙushe wasu hatsabiban ƴan bindiga da suka kashe sojoji huɗu.
Shugaba Bola Tinubu ya amince da alawus na ritaya ga shugabannin soja, ciki har da neman lafiya a waje, motoci da hadiman gida. Kungiyoyin likitoci sun nuna adawa.
Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya yi magana kan matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya. Ya ce dole ma'aikatar dabbobi da sulhu da 'yan bindiga za su inganta tsaro.
ISWAP ta kai hari kan sansanin soja a Damboa, ta kashe sojoji shida, ta banka wa sansanin wuta. Rikicin na tun 2009 ya halaka mutane 40,000 da raba miliyan biyu.
Sojojin Najeriya sun bayyana cewa Bello Turji yana buya a ramuka kamar beran daji sakamakon farmaki da suke kai masa ta sama da kasa a yankin Shinkafi.
Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda, ya yabawa dakarun sojojin Najeriya da sauran jami'an tsaro kan nasarorin da suka samu kan 'yan bindiga a jihar.
Jami’an tsaro sun kashe Sani Rusu, ɗan ta’addar Fulani a Tsafe a yayin wani samame, tare da ƙoƙarin kamo abokinsa, dillalin ƙwayoyi, Shamsu Danmali.
Rundunar sojojin saman Najeriya (NAF) ta yi ruwan bama-bamai kan 'yan ta'addan ISWAP a jihar Borno. Sojojin sun samu nasarar hallaka 'yan ta'adda masu tarin yawa.
Labarin Sojojin Najeriya
Samu kari