
Labaran Duniya







Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ba zai wakilci Najeriya a taron kasashen Commonwealth na 2024 da za a yi a Samoa kamar yadda aka tsara tun farko ba.

Rahoton ci gaban Najeriya (NDU) da Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa gwamnatin ta yi asarar Naira tiriliyan 13.2 na tallafin kudin kasashen waje (FX) a shekaru uku

Rahotanni sun bayyana cewa Dan wasan Najeriya Victor Boniface ya tsallake rijiya da baya a wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da shi a kasar Jamus.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya gama hutun da yake yi, ya dawo Najeriya. Olusegun Dada ya yi magana ya na mai nuna jirgin fadar shugaban Najeriya ya sauka.

Wasu 'yan bindiga dauke da makamai da ba a san ko su wanene ba sun hallaka dan takarar shugaban kasa a kasar Mozambique. Sun kuma hallaka lauyan 'yan adawa.

Aliko Dangote wanda ya samu karayar arziki tun daga shekarar da ta gabata ya sake zama mafi arziki a Afirka. Arzikinsa ya karu da $15bn zuwa Oktobar 2025.

Majalisar dattawan Kenya ta kada kuri'ar tsige mataimakin shugaban kasar, Rigathi Gachagua kan cin hanci da rashawa da wasu tuhume tuhume 10 da ya musanta.

An harbi tsohon ministan jihar Maharashtra ba adadia kirji a wajen ofishin dansa a Mumbai wanda ya yi silar mutuwarsa, a cewar kafafen yada labarai na Indiya.

Wani matukin jirgin saman Turkiyya ya mutu bayan ya yanke jiki a cikin jirgin a lokacin da yake tuki, lamarin da ya sa jirgin ya yi saukar gaggawa a birnin New York.
Labaran Duniya
Samu kari