Zaben jihohi
Hajiya Lubna Baba Gusau ta ayyana shiga takarar Sanatan Zamfara Ta Tsakiya a 2027, inda ta yi alƙawarin ba da fifiko ga mata, matasa, da kuma ci gaban mazaɓarta.
Tsohon Ministan Harkokin Waje Yusuf Maitama Tuggar ya ayyana takarar gwamnan Bauchi a 2027, inda ya lashi takobin gyara fannin noma da tsaro idan ya samu dama.
Gwamnoni 7 na Arewa, ciki har da Zulum da Buni, za su sauka daga mulki a 2027. Legit Hausa ta yi nazarin nasarorinsu da kuma makomar siyasarsu kafin barin gado.
Tsohon Minista Hadi Sirika ya ayyana neman kujerar Sanata a Katsina ta Arewa yau 24 ga Afrilu, 2026, sakamakon kiraye-kirayen al'ummar shiyyar Daura.
Jam'iyyar APC za ta fara sayar da fom din takara daga 25 ga Afrilu, 2026, sannan za ta gudanar da zaben fitar da gwani na shugaban kasa a ranar 23 ga Mayu.
Hukumar INEC ta fara shirin zaɓen 2027 a yau 23 ga Afrilu, 2026, inda ta ba jam'iyyun siyasa wa'adin kwanaki 38 domin gudanar da zaɓukan fitar da gwani.
Tsohon shugaban APC a Kwara, Bashir Bolarinwa, ya ayyana kudirinsa na tsayawa takarar gwamna, yana cewa yana da kwarewa da hangen nesa don magance matsalolin jiha.
Hukumar INEC ta matsar da ranar kammala yaƙin neman zaɓen gwamnan Osun zuwa 13 ga Agusta, 2026, bayan sauya ranar zaɓen zuwa 15 ga watan. An gargadi jam'iyyu.
Gwamna Abdullahi Sule ya ayyana Sanata Ahmed Wadada a matsayin wanda zai gaje shi a zaɓen 2027 domin ci gaba da mulkar jihar Nasarawa karkashin jam'iyyar APC.
Zaben jihohi
Samu kari