Labaran garkuwa da mutane
Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwa kan sace dalibai a makarantu da dama a jihohin Oyo da Borno, ta nemi a gaggauta ceto su cikin koshin lafiya.
Rahotanni daga Abuja sun nuna cewa jami'an tsaro sun tsaurara matakan tsaro a kewayen fadar shugaban kasa da ke Abuja gabanin fara zanga-zangar ceto dalibai.
Fitaccen dan fafutukar kafa kasar yarbawa, Sunday Igboho ya yi ikirarin cewa ya san 'yan siyasar da ke da hannu a tabarbarewar tsaro a Najeriya, ya gargade su.
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kama wasu dattawa biyu a cikin daji, sun bukaci a kai masu dauki. Dayan tsohon shugaban APC ne dayan malami.
Gwamnatin jihar Oyo ta ja hankalin masu amfani da kafafen sada zumunta kan sace dalibai, ta bukaci su rika tantance sahihan bayanai kafin su rika yada shi.
A labarin nan, za a ji bayanan sirri sun taimaka wa jami'an da ke jihar Yobe inda suka gano wani wuri da ake hada makamai tare da kwato wasu daga cikin makaman.
An tabbatar da mutuwar mutane biyar daga cikin masu ibada takwas da aka sace a cocin ECWA da ke Omugo, yankin Oro Ago, a karamar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara.
Kungiyar hadin kan yarbawa ta AYDM ta bayyana cewa gwamnonin Kudu Maso Yamma ne suka jawo tabarbarewar tsaron da ya jwo sace daliban makaranta a Oyo.
Tsohon gwamnan Ekiti, Ayo Fayose ya yi zargin cewa gwamnatin Seyi Makinde ce a jihar Oyo ta shirya sace dalibai da malamai don batawa Tinubu suna.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari