Labaran garkuwa da mutane
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Akwa Ibom ta tabbatar da cewa wasu ƴan bindiga sun yi garkuwa da direba da fasinjoji 18 a kan titi a jihar Akwa Ibom.
Rundunar 'yan sandan jihar Legas ta yi ram da wasu iyayen da su ka sa dansu a kasuwa domin su samu kudin ficewa daga kasar nan saboda matsin rayuwa.
Rundunar sojin Najeriya ta kai farmaki kan yan ta'adda a karamar hukumar Lau ta jihar Taraba, ta ceto mata biyu, yan bindiga sun kashe juna a yankin Wukari.
Rundunar yan sandan Kano ta damke matashi mai shekaru 22 Zakariyya Muhammad da zargin sace yar makocinsa mai shekaru biyu da rabi a duniya,tare da neman fansa.
Babban malamin addinin Kirista a jihar Zamfara, Mikah Sulaiman ya samu kubuta daga hannun yan bindiga bayan ya shafe makonni biyu a hannunsu a Zamfara.
Rahoto ya bayyana yadda wasu tsagerun 'yan bindiga suka yi garkuwa da wasu mutane 5 a jihar Niger, lamarin da ya yada hankalin al'ummar yankin da abin ya faru.
Rundunar 'yan sandan jihar Delta ta ce jami'anta sun samu nasarar hallaka wani mai garkuwa da mutane a jihar. 'Yan sandan sun kuma cafke takwarorinsa guda uku.
Yan bindiga sun turo sakon gargaɗi da barazana kwanaki kalilan bayan sun shiga garin Maidabino da ke karamar hukumar Ɗanmusa a jihar Katsina, sun sace mutum 50.
'Yan bindiga da suka sake alƙali Janet Gimba ta kotun gargajiya a Kaduna sun sake ta. Sun buƙaci kudin fansa N150 miliyan nan da kwana 6 ko su cutar da 'ya'yanta.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari