
Labaran garkuwa da mutane







Rundunar 'yan sandan Najeriya ta kai farmaki wata maboyar 'yan bindiga a jihar Akwa Ibom inda ta rusa maboyar tare da kwato miliyoyin Naira da makamai.

Dakarun sojin Najeriya sun yi nasarar kashe wani dan bindiga da ya shahara da kona gidaje da garkuwa da jama'a a Katsina. Soji sun yi raga raga da Yusuf Gwamna.

Mutanen gari a jihar Delta sun hadu sun tunkari 'yan bindiga masu garkuwa da mutane a jihar Delta. An kashe masu garkuwa uku bayan an musu jina jina.

Rundunar 'yan sandan Najeriya a jihar Legas sun kama wasu mutane biyu 'yan kasar Pakistan da suka yi amfani da jirgin sama wajen sace wani mutum a Kano.

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo ya bayyana cewa bokaye da malaman tsibbu ke yaudarar matasa da sunan kariya don su aikata miyagun laifuka.

Gwamnatin jihar Edo ta gano wasu gidaje da masu garkuwa da mutane suke boye wadanda suka sace a cikin gari. An rusa gidajen tare da gargadin al'umma.

Yan bindiga sun hallaka babban limamin cocin katolika bayan sun yi garkuwa da shi ranar Talata 4 ga watan Maris a yankin ƙaramar hukumar Kauru ta jihar Kaduna.

Rundunar ƴan sanda ta samu nasarar kama mutum 4 da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki cocin Katolika a jihar Edo, maharan sun yi garkuwa da limami da ɗalibi.

Rundunar 'yan sandan kasar nan ta shiga dimuwa bayan wasu da ake zargin 'yan fashi ne sun sace babban jamu'inta, Modestus Ojiebe a babban birnin tarayya.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari