Shafukan ra'ayi da sada zumunta
Rahotanni sun nuna cewa mazauna Kano na fuskantar rashin karfin hanyoyin sadarwa kamar tangarɗar kira da matsalar intanet kwanaki kaɗan kafin fara zanga zanga.
Kamfanin MTN ya sanar da rufe ofisoshinsa na fadin Najeriya daga yau Talata 30 ga watan Yulin 2024. Wannan na zuwa bayan kamfanin ya rufe layin daruruwan mutane.
Hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC) ta umarci kamfanonin sadarwa da su bude layukan da suka rufe saboda rashin sanya lambar NIN. Ta ja kunnen kwastomomi.
A yayin da daruruwan 'yan Najeriya ke kukan cewa kamfanin MTN ya rufe masu layinsu duk da cewa sun yi masa rijista da NIN. Mun yi bayanin hanyar bude layukan.
Kamfanonin sadarwa a Najeriya sun fara rufe layukan wayoyi wadanda ba a sanya musu lambar NIN ba. Ga hanyoyin yadda ake bude layin MTN da aka rufe.
Wasu fusatattun 'yan Najeriya da MTN ya rufewa layin waya a ranar Lahadi sun yiwa ofishin kamfanin tsinke a safiyar Litinin domin jin ba'asin abin da ya jawo hakan.
Hukumar hana yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) ta bayyana cewa ta kama wani matashi mai dalilin aure na bogi, inda aka gurfanar da shi kotu.
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta caccaki gwamnatin tarayya ta kama matashin dan tiktok, Junaidu Abdullahi bisa furucinsa a tiktok.
Mutane sun shiga wani irin yanayi bayan ganin wani bidiyo na wasu tsofaffi mata suna aikin leburanci inda wasu ke tausayawa musu ganin yadda shekarunsu suka ja.
Shafukan ra'ayi da sada zumunta
Samu kari