
Katsina







Dakarun sojojin saman Najeriya sun samu nasarar yin luguden wuta kan maboyar 'yan bindiga a jihar Katsina. Sojojin sun hallaka miyaginmasu yawa a farmakin.

Wasu miyagun 'yan bindiga sun sace wani matashi mahaddacin Al-Kur'ani a jihar Katsina. 'Yan bindigan sun sace shi ne tare da mahaifinsa da 'yan uwansa.

'Yan bindiga sun kafa sansani a Bakori, inda suke kai hare-hare. An rahoto cewa suna kokarin mamaye Tafoki, Faskari, Funtua da Danja, inda jama'a ke tserewa.

Gwamnatin Katsina ta fara rabon tallafi ga zawarawa 7,220 da mata marasa galihu, kowacce na samun buhun shinkafa da ₦10,000 don rage radadin rayuwa.

Dakarun sojin Najeriya sun yi nasarar kashe wani dan bindiga da ya shahara da kona gidaje da garkuwa da jama'a a Katsina. Soji sun yi raga raga da Yusuf Gwamna.

Wasu mutanen kananan hukumomi uku na jihar Katsina sun shiga yarjejeniyar yin sulhu da 'yan bindigan da suka addabe su. Sun fara ganin sabon sauyi.

Dakarun sojojin Najeriya na rundunar Operation Fansan Yanma sun samu nasarar dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane da 'yan bindiga suka yi a Katsina.

Sanata mai wakiltar Kudancin Katsina, Dandutse Mohammed Muntari, ya shawarci majalisar dattawa da kada ta amince da rage ko soke dakatarwar da aka yi wa Natasha.

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya ce ba za su yi sulhu da 'yan bindiga irinsu Turji ba, sai dai ya ce za a karbi tubansu idan suka ajiye makamai suka mika wuya.
Katsina
Samu kari