Kasashen Duniya
Shugaban Amurka, Donald Trump ya kama hanyar zuwa kasar China domin tattauna batun kasuwanci da harkokin tsaro duniya. Trump zai tattauna batun Iran a China.
Girgizar kasa mai karfin maki 4.6 ta afku kusa da Tehran a Jamhuriyar Iran, lamarin da ya jawo fargaba a yankunan da ke makwabtaka da babban birnin kasar.
Wani rahoto ya nuna cewa kasar Larabawa ta UAE ta kaddamar da hare-hare a kan Iran a lokacin da ake yakin Iran da Amurka da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya.
Aliko Dangote ya nuna sha'awar gina matatar mai ta dala biliyan 17 a Kenya ranar 10 ga Mayu, 2026, bayan ya kwatanta tattalin arzikin Kenya da na Tanzania.
A labarin nan, za a ji cewa kasashen Amurka da Iran sun sake samun rashin fahimta bayan bangarorin biyu sun ki amincewa da sharuddan sulhun da suka aika wa juna.
Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa Amurka za ta kwace kayan nukiliyar Iran, yana mai cewa rundunar Space Force na sanya ido sosai kan wuraren nukiliyar kasar.
Shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, ya yi tsokaci kan yakin kasarsa da Ukraine. Vladimir Putin ya nuna cewa nan ba da jimawa ba, yakin zai zo karshe.
Sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, ya gana da shugaban rundunar sojin kasar tare da bayar da sababbin umarnin ci gaba da farmakin soja kan abokan gaba.
Dubban Isra’ilawa sun gudanar da zanga-zanga domin nuna adawa da gwamnatin Benjamin Netanyahu da kuma hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kai wa kudancin Lebanon.
Kasashen Duniya
Samu kari