Jihar Kaduna
Gwamnatin Kaduna ta amince da nadin Bature Sunday Likoro a matsayin sabon Agwom Kamuru, bayan rasuwar Mai Martaba Yohanna Sidi Kukah a Disamba 2024.
Malamin addinin Kirista, Fasto Elijah Ayodele ya gargadi gwamnoni bakwai na Najeriya cewa samun wa’adin biyu a 2027 zai zama musu wahala saboda wasu dalilai.
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya gamsu da irin goyon da jam'iyyar APC ke samu. Ya bayyana cewa za ta samu kuri'u masu yawa a zaben shekarar 2027.
‘Yan bindiga sun kai hari ofishin ‘yan sanda a garin Zonkwa, da ke Kaduna, sun kashe jami’ai biyu; an ce sun kai farmaki ne don ‘yantar da wasu da aka kulle.
Rikici tsakanin masu hakar ma’adanai da ‘yan bindiga a Birnin Gwari, ya yi sanadin mutuwar mutane 7, yayin da mazauna suka bukaci gwamnati ta dauki mataki.
Wata babbar kotu a Kaduna ta rushe dokar ’yan sanda kan hana tarukan siyasa, ta umarci kwamishinan 'yan sanda ya biya ADC da SDP diyyar N15m saboda keta hakkoki.
Sojojin JTF sun kama ma’aurata da ake zargi da safarar makamai zuwa ‘yan ta’adda a Kaduna, sun gano harsasai 1,207 da ake shirin kaiwa Arewa maso Yamma.
‘Yan majalisar wakilai uku daga Kaduna sun sauya sheka daga PDP zuwa APC, yayin da Gwamna Uba Sani ya karrama su ta hanyar halartar zaman majalisar na yau.
Dan majalisar wakilai daga jihar Kaduna, Sadiq Ango Abdullahi, ya sanar da yin murabus dinsa daga jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya. Ya fadi dalilansa.
Jihar Kaduna
Samu kari