
Jihar Kogi







Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta ce za ta fitar da hujjoji da za su gaskta cewa shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya nemi ya yi lalata da ita.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta watau INEC ta sanar da shugaban Majalisar Dattawa, Godwill Akpabio cewa ta yi watsi da buƙatar yi wa Sanata Natasha Akpotu kiranye.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta ce nasara ce ga 'yan Najeriya bayan INEC ta yi watsi da ƙorafin yi mata kiranye. Ta ce an gama yaƙi ɗaya, saura biyu.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa watau INEC ta bayyana cewa bukatar da aka shigar da nufin tsige Sanata Natasha ba ta cika sharudɗan kundin tsarin mulki ba.

Tsohon Sanata mai wakiltar Adamawa ta Arewa, Elisha Ishaku Abbo, ya caccaki majalisa a kan yadda ake tafiyar da dambarwa Sanata Natasha Akpoti-Uduagan.

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan ta sake yin sabon zargi kan shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kan yunkurin yi mata kiranye.

Gwamnatin jihar Kogi ta musa zargin cewa ta kitsa yadda za ta kashe Sanata Natasha Akpoti. Haka zalika shugaban majalisa, Sanata Godswill Akpabio ya musa zargin.

Magoya bayan Sanata Natasha Akpoti Uduaghan sun nuna mata kauna bayan sun bijirewa dokar hana zirga zirgar da gwamnatin Kogi ta kakaba gabanin saukarta a jihar.

Ciyaman din Okehi da ke jihar Kogi ya sanya dokar hana fita a fadin karamar hukumar, saboda barazanar tsaro. An dauki matakin ne gabanin zuwan Sanata Natasha.
Jihar Kogi
Samu kari