
Jihar Kano







Jam'iyyar NNPP ta yi martani ga dan majalisarta, Kabiru Alhassan Rurum bayan suka da ya yi kan rusa masarautun Kano da Abba Kabir Yusuf ya yi a jihar.

Bayan dawowa sarautar Muhammadu Sanusi II za a daura auren dansa, Ashraf Adam Lamido Sanusi II da Sultana Mohammed Nazif a watan Agusta mai kamawa a Abuja.

Yayin da ake kuka saboda hauhawar farashin kayayyaki ciki har da na abinci, an fara samun saukin farashin hatsi a kasuwar Dawanau, kamar yadda Legit ta taro.

Wasu daga cikin jaruman Kannywood sun fice daga NNPP zuwa APC a jihar Kano. Rabi'u Daushe, Hauwa Waraka, Alhaji Habu Tabule na cikin wadanda Barau Jibrin ya karba.

Gamayyar sarakunan gargajiya a Kudu maso Gabashin Najeriya sun roki Shugaba Bola Tinubu alfarmar samar da sababbin jihohi a yankin da suke da guda biyar.

Rundunar 'yan sandan Kano ta ce an yi zaman taro na musamman a kan shirin gudanar da zanga zanga, inda aka gana da dukkanin shugabannin tsaro a jihar.

Duk da matasan kasar nan sun bayyana cewa za su gudanar da zanga-zangar lumana a cikin kwanaki 10, yan kasuwa sun dauki matakin ba wa shagunansu da ke Kano tsaro.

Al'ummar wasu unguwanni daga jihar Kano sun kai wa Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ziyara domin nuna goyon bayansu gare shi tare da masa addu'o'i.

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya yi maganganun da suka tayar da kura tun dawowarsa mulki. An caccaki sarkin bisa kalamansa da ake ganin hujja ne a kansa.
Jihar Kano
Samu kari